ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu

by Abubakar Abba
1 year ago
Kaji

A cikin halin da ake ciki yanzu, akasarin masu kiwon Kajin gidan gona, na ci gaba da fuskantar kalubalen da ya hada da rage yawan samun masu sayen Kwai.

Kazalika, suna fuskantar kalubalen dakatar da wasu shirye-shiryen gwamnati, kamar na bai wa daliban makarantar firamare Kwai da sauran shirye-shiryen da gwamnatin ta kirkiro, wadanda suka shafi bangaren bayar da Kwan.

  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • Ina Dalilin Da Ya Sa Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin Ke Samun Bunkasuwa Mai Dorewa Ba Tare Da Tangarda Ba?

Kusan za a iya cewa, wadannan matsaloli da masu kiwon Kajin gidan gona ke fuskanta, na kara ta’azzara ne sakamakon ba su kayan ayyukan da za su iya adana Kwan har zuwa wani dogon lokaci, musamman duba da yanayin zafin da ake fuskanta a fadin wannan kasa, ya kara tabarbara al’amuran kiwon baki-daya.

ADVERTISEMENT

Wadannan matsaloli, sun jawo wa masu kiwon Kajin na gidan gona, sayar da Kwansu cikin farashi mai rahusa, musamman don guje wa tabka asara.

Ya danganta da yadda girman Kwan yake, misali, a babban birnin tarayyar Abuja, a kananan shaguna yanzu, ana sayar da duk kiret daya daga tsakanin Naira 5,000 zuwa Naira 6,500.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Bugu da kari, saboda karancin masu sayen Kwan, musamman sakamakon matsin tattalin arziki da ake fama da shi, ana kara samun masu sayen Kwan don amfani da shi, wanda hakan ya sanya ake ci gaba da samun Kwan da ba a sayar ba.

Misali, a makwanni biyu da suka gabata a garin Jos, an samu matukar raguwar farashin Kwan, inda ake sayar da shi kasa da Naira 3,900 zuwa Naira 4,000.

Sai dai, a wannan makon an dan samu karin farashin, wanda ya kai daga Naira 4,200 zuwa 4,300.

Daya daga cikin irin wadannan masu kiwon Kajin na gidan gona, Muhammad Bello Ibrahim, ya bayyana bacin ransa kan yadda wannan matsala ke ci gaba da faruwa.

“Masu sana’ar kiwon Kajin a yanzu haka, suna ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan,” in ji Bello.

Ya ci gaba da cewa, a baya; a karkashin shirye-shiryen ciyarwa na gwamnati, ana karfafa wa wasu jihohin sayen Kwan da ake bai wa ‘yan makarantar firamere, domin amfanin marasa lafiya da aka kwantar a asibiti da kuma amfanin wadanda ake tsare da su a gidan gyaran hali, amma kusan yanzu, shirye-shiryen sun tsaya cak.

Bisa wani bincike da aka gudanar a garin na Jos, duk da raguwar da aka samu na farashin Kwan, ana ci gaba da fuskatar karancin masu saye, wanda kuma hakan ya sa ake samun kwantan Kwan.

Hakan na kuma faruwa ne a yayin da ake ci gaba da fuskantar tsananin zafi, a jihohin kasar ciki har da garin na Jos.

Wata mai kiwon Kajin gidan gona a Jihar Filato, Nanji Gambo-Oke, ta sanar da cewa, kiwon Kajin a jihar, na fuskanta babban kalubale.

A cewar tata, kashi 80 cikin dari na Kwan da ake kyankyashewa a jihar, makwabtan jihar ne ke zuwa saye, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

Ta kara da cewa, a bangaren gwamnatin jihar kuma tana nuna halin ko in kula dangane da kwantan Kwan da masu kiwon a jihar ke ci gaba da samu.

“Babu wani dauki da masu kiwon Kajin gidan gonar a jihar ke samu daga bangaren gwamnatin jihar, wanda hakan ke ci gaba da jefa su cikin halin tsaka mai wuya”, in ji Nanji.

Sai dai, Shugabar Kungiyar Masu Kiwon Kajin Gidan Gonar, reshen jihar Madam Shinkur Angela Jima, ta sanar da cewa, gwamnatin jihar na nuna goyon baya ga fannin.

Ta kara da cewa, a yanzu haka, gwamnatin na kokarin samar da tsare-tsaren da za ta tallafa wa masu kiwon a jihar.

Bugu da kari, a Jihar Neja ma, masu kiwon Kajin na ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan da kuma rashin samun kayan aiki na zamani, wanda hakan ke jawo lalacewar Kwan nasu.

Kaji
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.