ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu

by Abubakar Abba
1 year ago
Kaji

A cikin halin da ake ciki yanzu, akasarin masu kiwon Kajin gidan gona, na ci gaba da fuskantar kalubalen da ya hada da rage yawan samun masu sayen Kwai.

Kazalika, suna fuskantar kalubalen dakatar da wasu shirye-shiryen gwamnati, kamar na bai wa daliban makarantar firamare Kwai da sauran shirye-shiryen da gwamnatin ta kirkiro, wadanda suka shafi bangaren bayar da Kwan.

  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • Ina Dalilin Da Ya Sa Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin Ke Samun Bunkasuwa Mai Dorewa Ba Tare Da Tangarda Ba?

Kusan za a iya cewa, wadannan matsaloli da masu kiwon Kajin gidan gona ke fuskanta, na kara ta’azzara ne sakamakon ba su kayan ayyukan da za su iya adana Kwan har zuwa wani dogon lokaci, musamman duba da yanayin zafin da ake fuskanta a fadin wannan kasa, ya kara tabarbara al’amuran kiwon baki-daya.

ADVERTISEMENT

Wadannan matsaloli, sun jawo wa masu kiwon Kajin na gidan gona, sayar da Kwansu cikin farashi mai rahusa, musamman don guje wa tabka asara.

Ya danganta da yadda girman Kwan yake, misali, a babban birnin tarayyar Abuja, a kananan shaguna yanzu, ana sayar da duk kiret daya daga tsakanin Naira 5,000 zuwa Naira 6,500.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Bugu da kari, saboda karancin masu sayen Kwan, musamman sakamakon matsin tattalin arziki da ake fama da shi, ana kara samun masu sayen Kwan don amfani da shi, wanda hakan ya sanya ake ci gaba da samun Kwan da ba a sayar ba.

Misali, a makwanni biyu da suka gabata a garin Jos, an samu matukar raguwar farashin Kwan, inda ake sayar da shi kasa da Naira 3,900 zuwa Naira 4,000.

Sai dai, a wannan makon an dan samu karin farashin, wanda ya kai daga Naira 4,200 zuwa 4,300.

Daya daga cikin irin wadannan masu kiwon Kajin na gidan gona, Muhammad Bello Ibrahim, ya bayyana bacin ransa kan yadda wannan matsala ke ci gaba da faruwa.

“Masu sana’ar kiwon Kajin a yanzu haka, suna ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan,” in ji Bello.

Ya ci gaba da cewa, a baya; a karkashin shirye-shiryen ciyarwa na gwamnati, ana karfafa wa wasu jihohin sayen Kwan da ake bai wa ‘yan makarantar firamere, domin amfanin marasa lafiya da aka kwantar a asibiti da kuma amfanin wadanda ake tsare da su a gidan gyaran hali, amma kusan yanzu, shirye-shiryen sun tsaya cak.

Bisa wani bincike da aka gudanar a garin na Jos, duk da raguwar da aka samu na farashin Kwan, ana ci gaba da fuskatar karancin masu saye, wanda kuma hakan ya sa ake samun kwantan Kwan.

Hakan na kuma faruwa ne a yayin da ake ci gaba da fuskantar tsananin zafi, a jihohin kasar ciki har da garin na Jos.

Wata mai kiwon Kajin gidan gona a Jihar Filato, Nanji Gambo-Oke, ta sanar da cewa, kiwon Kajin a jihar, na fuskanta babban kalubale.

A cewar tata, kashi 80 cikin dari na Kwan da ake kyankyashewa a jihar, makwabtan jihar ne ke zuwa saye, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

Ta kara da cewa, a bangaren gwamnatin jihar kuma tana nuna halin ko in kula dangane da kwantan Kwan da masu kiwon a jihar ke ci gaba da samu.

“Babu wani dauki da masu kiwon Kajin gidan gonar a jihar ke samu daga bangaren gwamnatin jihar, wanda hakan ke ci gaba da jefa su cikin halin tsaka mai wuya”, in ji Nanji.

Sai dai, Shugabar Kungiyar Masu Kiwon Kajin Gidan Gonar, reshen jihar Madam Shinkur Angela Jima, ta sanar da cewa, gwamnatin jihar na nuna goyon baya ga fannin.

Ta kara da cewa, a yanzu haka, gwamnatin na kokarin samar da tsare-tsaren da za ta tallafa wa masu kiwon a jihar.

Bugu da kari, a Jihar Neja ma, masu kiwon Kajin na ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan da kuma rashin samun kayan aiki na zamani, wanda hakan ke jawo lalacewar Kwan nasu.

Kaji
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

Cibiyoyin Hada-Hadar Kudi Na Ketare Suna Da Kyakkyawar Fata Game Da Kasuwar Lamuni Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.