• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

by Abubakar Abba
6 months ago
in Tattalin Arziki
0
Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wake na daya daga cikin amfanin gonar da aka dakatar da shigar da da shi daga Nijeriya zuwa Tarayyar Turai.

Wasu kwararru sun yi gargadin cewa, akwai yiwuwar farashin Wake ba zai sauka ba a wannan kasa da muke ciki.

  • Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya
  • Nazari Kan Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Wake A Nijeriya

Kazalika, Cibiyar Kula da Fitar da Kayayyaki Kasashen Waje ta Kasa (NEPC) ta sanar da cewa, Nijeriya na noma Wake mai dimbin yawa; wanda ya kai kimanin kashi 58 cikin 100 na yawan wanda ake bukata a duniya.

Sai dai, wasu matsaloli da suka hada da ayyukan ‘yan bindigar daji, yawan rikice-rikice a tsakanin manoma da makiyaya da sauran makamantansu, an danganta su a matsayin manyan kalubalen da ke jawo rashin noman Waken da dama a Nijeriya.

Bugu da kari, akwai kuma kalubalen rashin kayan aiki; da suka hada da samar da wurin adana shi da rashin yin amfani da dabarun zamani, wanda hakan ya jawo rashin samar da wadatuwar sa a fadin wannan kasa.

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Shugaban Kungiyar Manoma na Kasar, reshen Jihar Kano (AFAN); Alhaji Abdulrasheed Magaji Rimin Gado ya sanar da cewa, sauyin yanayi da kuma matsalar rashin tsaro, sun yi matukar taka muhimmiyar rawa wajen kawo raguwar noman wannan Wake.

An ruwaito cewa, Jamhuriyar Nijar; na tura kimanin kashi 45 cikin 100 na Waken da take nomawa zuwa wasu jihohin Arewacin Nijeriya, inda ake hada-hadar kasuwacninsa ta hanyar musayar Naira da kuma takardar kudin CFA, wanda hakan ko kadan baya taimakawa wannan fanni.

Magaji ya ci gaba da cewa, manyan dillalansa ba sa iya shigo da shi cikin wannan kasa, sakamakon matsalar samun kudaden musaya da ba sa iya samu.

Ya kara da cewa, lamuran na ci gaba da kara munana; musamman idan aka yi la’akari da wani rahoto da ya riske mu da ke nuna cewa, Jamhuriyar ta Nijar ta dakatar da fitar da amfanin gona daga kasar zuwa wasu kasashe, ciki har da Nijeriya.

A cewarsa, hakan ba zai bari farashinsa da sauran kayan amfanin gona su ragu ba.

Ya sanar da cewa, akwai matukatar bukatar a bai wa noman rani muhimmanci, musamman don cike gibin da aka samu a noman damina na bana.

Kazalika, ya sanar da cewa, ya zama wajibi gwamnati ta kayyade farashi, musamman a kan Wake domin samar da wadatuwarsa; cikin kuma farashi mai sauki.

Shi ma, wani babban dila a Kasuwar Hatsi ta kasa da kasa a Kasuwar Dawanau ta Jihar Kano, Alhaji Musa Gawuna ya bayyana cewa; ba a noman Wake da yawa, duk kuwa da matukar bukatar da ake da shi.

A cewarsa, wasu manoman; musamman na Waken, na kauracewa gonakinsu, saboda yawan samun rikice-rikicen manoma da makiyaya, wanda hakan ya dakatar da manoman daga yin nomansa kamar yadda aka yi tsammani.

Rahotannin sun ce, mahukuntan soji na kasar Nijar, sun dakatar da fitar da Shinkafa da sauran amfanin gona zuwa sauran kasashen duniya.

Sun dauki wannan matakin ne, biyo bayan barazanar da kungiyar ECOWAS ta yi wa mahukuntan kasar na cewa, tilas ne su mayar da kasar kan turbar mulkin dimokradiyya; bayan juyin mulkin da suka yi a kasar a shekarar da ta gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Wake
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

Next Post

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

6 days ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

Nijeriya Ta Tafka Asarar Dala Biliyan 1.5 Sakamakon Watsi Da Fannin Kiwon Dabbobi

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.