• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Wake A Nijeriya

by Abubakar Abba
9 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Nazari Kan Lokacin Da Ya Fi Dacewa A Shuka Wake A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akasari, an fi so manomi ya shuka Wake a watan Okutoba a Kudancin wannan kasa, inda kuma a Arewacin Nijeriya aka fi so a shuka Waken a watan Agusta.

Gyaran Gona:

Wanda zai noma Wake, idan bai mallaki gona tasa ta kansa ba; zai iya hayar wata gonar, musamman ganin cewa a cikin kwanaki kadan zai iya girbe shi, idan manomi yana da Naira 20,000; zai iya karbar gona haya, amma ya danganta da irin wajen da gonar take.

  • Sin Ba Za Ta Canza Matsayarta Game Da Mayar Da Hankali Kan Kasashe Masu Tasowa Ba
  • CBN Ya Ƙi Amince Wa Da Umarnin Majalisa Kan Dakatar Da Amfani Da Tsofaffin Naira

Har ila yau, ba a so manomi ya sake shuka Wake a gonar da ya noma shi, har sai bayan tsawon shekara uku, haka a kowace irin kasar noma; ana iya shuka shi.

Lokacin Shuka Shi:

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Ana bukatar manomi idan ya tashi shuka Wake, ya shuka shi a ramin da zurfinsa ya kai daga mita daya zuwa mita biyu, inda kuma ake bukatar a kowane rami daya; a shuka Irinsa guda uku. Haka nan, ana so a bayar da sararin da ya kai daga mita 24 zuwa mita 30 a kowane layi guda, sannan kuma; Wake na fara rubawa ne a cikin kasar noma bayan kwana shida da shuka shi.

Ban Ruwa:

Waken da aka shuka na saurin rubawa a cikin kasar noman da aka shuka shi, haka nan yana iya girma ko da ba a yi masa ban ruwa ba, kazalika; Wake na bukatar ruwan saman da ya kai kimanin kwana talatin ana yin sa a jere.

Har ila yau, Irin nomansa bai cika bukatar ruwa sosai ba, domin ruwan zai iya kashe shi ta hanyar rubewar saiwowinsa, sai dai idan ruwan sama ya tsaya baki-daya, ana bukatar a yi masa ban ruwa, kazalika ba a bukatar manominsa ya rika yi masa ban ruwa a kan ganyensa; domin zai iya lalacewa.

Zuba Taki:

Ana bukatar manomin Wake ya yi amfani da takin gargajiya, musamman idan kasar noman da aka shuka shi ba ta dauke da wasu sinadarai, musamman don kara wa kasar noman inganci, har ila yau, manomi zai kuma iya zuba masa takin zamani.

Ba Shi Kariya Daga Kamuwa Daga Cututtuka Ko Kwari:

Ana bukatar manomi ya tabbatar da kare shi daga kamuwa daga kwayoyin cuta da kuma kwarin da ke yi masa illa, musamman don kauce wa tabka asara.

Lokacin Girbe Shi:

Akasari, Wake na kammala nuna ne a cikin kwana 80 ko kuma sama da haka, ya danganta da irin nau’in Irin da aka shuka; haka nan kuma ba a so a bata lokaci wajen girbe shi.

Kasuwancinsa:

Za ka iya sayar wa da mata ko mazan da ke yin sana’arsa, haka zalika; za ka iya sayar da akasarinsa a manyan shaguna ko kuma ga manyan diloli, sannan kuma za ka iya yin tallansa a kafar yanar Gizo ko fitar da shi zuwa kasashen waje da sauran su, inda a a baya; farashin buhu daya na Waken ke kai wa kimanin Naira 70,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NomaWake
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ce Ummul Haba’isin Ruruta Wutar Rikicin Jam’iyyun Adawa Don Samun Nasara A 2027 — NNPP

Next Post

Isra’ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

7 days ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

7 days ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

4 weeks ago
Next Post
Isra’ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

Isra'ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.