ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Wake

Wake na daya daga cikin cimar akasarin ‘yan Nijeriya, duba da cewa yana daya daga cikin abinci mai gina jikin Dan’adam. Wannan dalili ne ya sa a kauyuka da birane al’umma da dama ke noman sa, domin amfanin gida da kuma sayarwa a kasuwanni.

Sai dai, wasu manoman ba sa bin hanyar da ta dace wajen noman wannan Wake. Domin kuwa, a Nijeriya girbin da ake samu har yanzu bai wuce kasa da tan 0.2 a kowace hekta daya, duk da cewa kuma; masu yin nomana Waken ta hanyar da ta dace, sukan iya girbe kimanin tan 2 a kowace hekta guda.

Watannin da suka fi dacewa a noma Wake a kasar nan, na farawa ne daga watan Mayu zuwa na Yuni.

ADVERTISEMENT

Kazalika, dangane da yanayin kakar damina; ana kuma yin nomansa daga watan Mayu, Yuni da kuma na Yuli.

Babu shakka, nomansa a cikin wadannan watanni; zai sa ya samu isasshe ko kuma wadataccen ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Haka zalika, wadanda ke noman wannan Wake a lokacin rani; za su iya shuka Irinsa a kowane irin lokaci.

Watannin da suka fi dacewa a shuka Wake a Nijeriya sun hada da watan Afirilu, Mayu, Yuni, Juli, Augusta, Satumba har kuma zuwa Disamba.

 

Watan Afirilu:

A kudancin Nijeriya, ana fara shuka Irin Wake a watan Afirilu, sakamakon cewa a wannan wata ne ake fara yin ruwan sama.

Har ila yau, a cikin watan ne kuma Irin Waken da aka shuka; galibi ba a cika samun wata matsala kamar ta kwarin da ke lalata amfanin gona ko wani abu makamancin haka ba.

 

Watan Mayu:

A Nijeriya, musamman a yankunan da suke da dausayi ne ake fara samun ruwan sama, wanda hakan ya sa watan ya kasance, lokacin da ya fi dacewa a shuka Irin Waken.
Kazalika, a cikin watan ne Waken da aka shuka zai yi girma sosai; domin ba a cika samun kwarin da suke lalalata amfanin gonar ba.

 

Watan Yuni:

Shi ma wannan watan, na daya daga cikin watan da ya dace a shuka Irin Wake a kudancin Nijeriya da kuma Arewacin kasar. Domin kuwa, a cikin watan ba a cika samun kwarin da ke lalata amfanin gonar ba.

 

Watan Yuli:

Shi ma wannan watan, na daya daga cikin watannin da suka dace a noma Wake, musamman a kudancin wannan kasa, a kuma cikin watan; ba a cika samun kwarin da ke lalata amfanin ba.

Watan Augusta:

Musamman a kudancin Nijeriya, wannan watan na da matukar kyau a shuka Irin Wake, sai dai ana kuma bukatar manomi ya kasance ya tanadi kayan ban ruwan da zai yi wa Waken.

Haka nan, a Arewacin Nijeriyar; ganin cewa a watan ne ake samun ruwan sama mai yawa, watan ya kasance mafi kyau na shuka Irin Waken.

 

Watannin Satumba zuwa na Disamba:
Zai iya yiwuwa, Wake ya girma a cikin wadannan watanni har zuwa cikin watan Oktoba.

Daga watan Satumba zuwa Disamba, nan ne kakar rani ke fara kunnu kai; inda kuma za a iya samun bullar kwarin da ke lalata amfanin gona, wanda a cikin watannin ne kuma ake so manomi ya rika amfani da magungunan kashe kwari.

Wake
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Wake
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Waiwaye Game Da Shirin “Kauyuka Dubu Goma” Da Daidaita Yanayin Kauyukan Kasar Sin

Takaitaccen Nazari A Kan Noman Nau’o’in Abinci 7

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.