• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Gasar Wasannin Asiya Ta Hangzhou Ta Samu Cikakken Goyon-Baya Daga Al’ummun Kasashen Asiya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hangzhou
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

An kaddamar da gasar wasannin motsa jiki ta kasashen Asiya karo na 19 wato Asian Games da daren ranar 23 ga watan Satumba a birnin Hangzhou na lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin, wanda ya kasance karo na uku da kasar ta karbi bakuncin gasar wasannin Asiya, bayan gudanar da irin ta a shekara ta 1990 a Beijing, da shekara ta 2010 a Guangzhou.

A matsayinta na gagarumar gasar wasannin motsa jiki ta kasashen Asiya, gasar tana hade da burikan al’ummun Asiya, a fannonin samar da zaman lafiya, da inganta hadin-gwiwa da nuna hakuri. A cikin jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a wajen shagalin maraba da zuwan baki ‘yan kasashen waje na bikin bude gasar, ya bayyana fatansa ga gasar a wannan karo, wato tabbatar da zaman lafiya da karfafa hadin-gwiwa da kara nuna hakuri ta hanyar gudanar da wasannin motsa jiki. A shekaru goman da suka gabata, tattalin arzikin nahiyar Asiya ya habaka cikin sauri, wanda ya dauki kaso 40 bisa dari na tattalin arzikin duk duniya. Gasar wasannin Asiya ta ganewa idanunta gami da bayar da babbar gudummawa wajen kirkiro “al’ajabin Asiya”. Amma har yanzu akwai wasu kasashen sauran nahiyoyi, dake yunkurin tunzura rikici da lalata zaman lafiya da kwanciyar hankali a nahiyar Asiya, al’amarin ya sa al’ummun nahiyar suke matukar fatan samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ta hanyar gudanar da gasar wasannin motsa jiki. Ana iya cewa, gasar wasannin Asiya ta Hangzhou ta bana, na dauke da irin wannan fata na jama’ar nahiyar Asiya.

A tsawon kwanaki 16 na gasar, ba gagaruman gasanni kawai jama’a za su kalla ba, har ma za su iya kara fahimtar yadda ake kokarin inganta hadin-gwiwa da sada zumunta. Duba da cikakken goyon-bayan da al’ummun kasashen Asiya ke samarwa, babu shakka gasar wasannin Asiya ta Hangzhou za ta bayar da sabuwar gudummawa ga ci gaban gasar wasannin Olympics da karfafa hadin-gwiwa da zumunci tsakanin al’ummun kasashen Asiya. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsiyaJapan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiya Ta Nemi ‘Yan Adawa Su Rungumi Kaddara Kan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnan Bauchi

Next Post

Gobarar Man Fetur Ta Hallaka Mutum 34 A Jamhuriyar Benin

Related

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

5 hours ago
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

6 hours ago
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela
Daga Birnin Sin

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

7 hours ago
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

8 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

9 hours ago
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

9 hours ago
Next Post
Gobarar Man Fetur Ta Hallaka Mutum 34 A Jamhuriyar Benin

Gobarar Man Fetur Ta Hallaka Mutum 34 A Jamhuriyar Benin

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.