• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fadar shugaban kasa ta yi karin haske game da wasan kwaikwayo da rudanin shari’a da ke tattare da gazawar jami’an tsaro wajen cafke Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, duk da kokarin da aka yi.

Mai Magana Da Yawun Shugaban Kasar, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan yayin da yake magana a wani shirin zamantakewa da tattalin arziki na gidan talabijin na Channels, mai suna ‘Inside Sources with Laolu Akande’.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Onanuga ya bayyana kalubale na musamman da ke tattare da kusancin Bello da magajinsa, Gwamna Usman Ododo, wanda ke da kariyar tsarin mulki.

LEADERSHIP ta tunatar da cewa, a watan Afrilu, Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta bayyana cewa ana neman Bello ne bisa zarginsa da aikata laifukan kudi da suka hada da Naira biliyan 80.2. Duk da cewa hukumar EFCC ta yi yunkurin cafke tsohon gwamnan, amma yunkurin ya ci tura, inda rahotanni suka ce Ododo ya kare Bello tare da ba wa gwamnan mafaka a masaukinsa.

Ya kara da cewa, yayin da hukumar EFCC ta dukufa wajen gurfanar da Bello a gaban kuliya, kariyar da aka bai wa Gwamna Ododo a karkashin tsarin mulki na dagula duk wani yunkuri na kama tsohon gwamnan.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ita ce matsalar domin idan shi (Bello) ya zauna a gidan Gwamna Ododo, ‘yan sanda ba za su iya yin komai ba saboda za su keta wannan rigar da gwamna ke da ita.

“Kamar jami’in diflomasiyya ne da yake da kariya, don haka ba za ku iya yin komai game da shi ba. Kun tuna a Burtaniya lokacin da suke neman mutumin nan Wikileaks, sai ya je ya buya a wani ofishin jakadanci a Biritaniya, ba abin da su ( jami’an tsaro) za su iya yi, dole haka nan suka bar shi a can. Ina tsammanin daga baya ne ya fito suka kama shi,” Onanuga ya fadi haka yayin da yake tabbatar da rashin ikon EFCC.

Tsohon gwamnan Jihar Kogi, wanda ya yi mulki daga shekarar 2016 zuwa Mayu 2024, ya kasa gurfana a gaban kotu duk da yawan sammaci da kuma dage sauraren karar da aka yi masa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCKogiYahaya Bello
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashin Da Ya Kware Wajen Satar Na’urorin AC A Kotu, Ya Fada Komar ‘Yansanda

Next Post

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

3 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

4 months ago
Next Post
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

May 28, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

May 28, 2025
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

May 28, 2025
Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

May 28, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

May 27, 2025
Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

May 27, 2025
Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

May 27, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.