ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Kogi

Fadar shugaban kasa ta yi karin haske game da wasan kwaikwayo da rudanin shari’a da ke tattare da gazawar jami’an tsaro wajen cafke Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, duk da kokarin da aka yi.

Mai Magana Da Yawun Shugaban Kasar, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan yayin da yake magana a wani shirin zamantakewa da tattalin arziki na gidan talabijin na Channels, mai suna ‘Inside Sources with Laolu Akande’.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Onanuga ya bayyana kalubale na musamman da ke tattare da kusancin Bello da magajinsa, Gwamna Usman Ododo, wanda ke da kariyar tsarin mulki.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta tunatar da cewa, a watan Afrilu, Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta bayyana cewa ana neman Bello ne bisa zarginsa da aikata laifukan kudi da suka hada da Naira biliyan 80.2. Duk da cewa hukumar EFCC ta yi yunkurin cafke tsohon gwamnan, amma yunkurin ya ci tura, inda rahotanni suka ce Ododo ya kare Bello tare da ba wa gwamnan mafaka a masaukinsa.

Ya kara da cewa, yayin da hukumar EFCC ta dukufa wajen gurfanar da Bello a gaban kuliya, kariyar da aka bai wa Gwamna Ododo a karkashin tsarin mulki na dagula duk wani yunkuri na kama tsohon gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ita ce matsalar domin idan shi (Bello) ya zauna a gidan Gwamna Ododo, ‘yan sanda ba za su iya yin komai ba saboda za su keta wannan rigar da gwamna ke da ita.

“Kamar jami’in diflomasiyya ne da yake da kariya, don haka ba za ku iya yin komai game da shi ba. Kun tuna a Burtaniya lokacin da suke neman mutumin nan Wikileaks, sai ya je ya buya a wani ofishin jakadanci a Biritaniya, ba abin da su ( jami’an tsaro) za su iya yi, dole haka nan suka bar shi a can. Ina tsammanin daga baya ne ya fito suka kama shi,” Onanuga ya fadi haka yayin da yake tabbatar da rashin ikon EFCC.

Tsohon gwamnan Jihar Kogi, wanda ya yi mulki daga shekarar 2016 zuwa Mayu 2024, ya kasa gurfana a gaban kotu duk da yawan sammaci da kuma dage sauraren karar da aka yi masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.