ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
EFCC

Hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta sanar da samun nasarar kama wasu mutum biyu da suka damfari wani dattijo Alhaji Aminu Dantata da tsohon minista Alhaji A.T. Gwarzo.

Bugu da kari, hukumar ta kwato Naira miliyan 5, daga hannun wadanda aka kama din sun damfari daga hannun hamshakin dan kasuwar, ciki har da Naira miliyan daya mallakin tsohon ministar bayan gurfanar da su gaban kotu.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman kotun, lauyan masu shigar da kara Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bayyana cewa Bukar Galadima da Sulyman Ahmed sun shirya tare da aiwatar da wani shiri na damfarar wadanda abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

Bukar Galadima ya yi sojan gona da sunan Tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Abba Gana, inda nuna tsohon ministan ba shi da lafiya, ya kuma nemi taimakon Aminu Dantata, inda ya bukaci Naira miliyan 5 domin a yi masa magani, daga nan sai Dantata ya umarce shi da ya ba shi bayanan asusun ajiyarsa. A maimakon ya bayar da nasa, Galadima ya bayar da bayanan matarsa, Sadiyya Abba.

Daga nan ne dan kasuwar ya mika Naira miliyan 5 zuwa asusun ajiyar kudi domin tallafa wa wanda ke jinya.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

Daga baya, da Dantata ya tuntubi tsohon ministan don duba lafiyarsa, sai ya gane cewa an zambace shi, ya kai karar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, inda ta fara bincike.

An kama mutanen biyu ne kuma aka gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 24 da ke Kano.

Alkaliyar kotun ya yanke wa ’yan damfara hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru hudu a kowane makon da ya gabata.

An tuhumi mutanen biyu da laifin hada baki, damfara, cin amana, da kuma zamba.

Lokacin da aka karanta Rahoton Bayanin Farko, dukkansu sun amsa laifukan guda hudu. Lauyan masu gabatar da kara Barista Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bukaci a yi masa shari’a a karkashin sashe na 129 (8) na shari’ar ACJL 2019. Daga nan kuma aka yanke musu laifin.

Alkaliyar Kotun Majistare Umma Sani Kurawa ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin daurin watanni shida a gidan yari saboda samun su da laifin hada baki (ko tarar Naira 30,000 kowannensu), watanni uku kan aikata laifuka (ko tarar Naira 20,000 kowanne), shekara daya saboda zamba (ko kuma tarar Naira 20,000 kowanne), tarar Naira 30,000 kowanne), da watanni shida kan laifin karya cin amana (ko tarar Naira 20,000 kowanne).

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

Hukumar ta lura da cewa, duk da cewa babu wani korafi da tsohuwar ministar ya yi, an gano shirin nasu ne a yayin gudanar da bincike.

Hukumar ta kwato kudaden da aka damfara kuma za a mayar wa Aminu Dantata da Alhaji A.T. Gwarzo.

Dukkanin wadanda aka yankewa hukuncin kuma an bukaci su sanya hannu kan takardar yarjejeniya don su zamto masu kyawawan halaye.

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

EFCC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.