ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
EFCC

Hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta sanar da samun nasarar kama wasu mutum biyu da suka damfari wani dattijo Alhaji Aminu Dantata da tsohon minista Alhaji A.T. Gwarzo.

Bugu da kari, hukumar ta kwato Naira miliyan 5, daga hannun wadanda aka kama din sun damfari daga hannun hamshakin dan kasuwar, ciki har da Naira miliyan daya mallakin tsohon ministar bayan gurfanar da su gaban kotu.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman kotun, lauyan masu shigar da kara Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bayyana cewa Bukar Galadima da Sulyman Ahmed sun shirya tare da aiwatar da wani shiri na damfarar wadanda abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

Bukar Galadima ya yi sojan gona da sunan Tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Abba Gana, inda nuna tsohon ministan ba shi da lafiya, ya kuma nemi taimakon Aminu Dantata, inda ya bukaci Naira miliyan 5 domin a yi masa magani, daga nan sai Dantata ya umarce shi da ya ba shi bayanan asusun ajiyarsa. A maimakon ya bayar da nasa, Galadima ya bayar da bayanan matarsa, Sadiyya Abba.

Daga nan ne dan kasuwar ya mika Naira miliyan 5 zuwa asusun ajiyar kudi domin tallafa wa wanda ke jinya.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

Daga baya, da Dantata ya tuntubi tsohon ministan don duba lafiyarsa, sai ya gane cewa an zambace shi, ya kai karar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, inda ta fara bincike.

An kama mutanen biyu ne kuma aka gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 24 da ke Kano.

Alkaliyar kotun ya yanke wa ’yan damfara hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru hudu a kowane makon da ya gabata.

An tuhumi mutanen biyu da laifin hada baki, damfara, cin amana, da kuma zamba.

Lokacin da aka karanta Rahoton Bayanin Farko, dukkansu sun amsa laifukan guda hudu. Lauyan masu gabatar da kara Barista Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bukaci a yi masa shari’a a karkashin sashe na 129 (8) na shari’ar ACJL 2019. Daga nan kuma aka yanke musu laifin.

Alkaliyar Kotun Majistare Umma Sani Kurawa ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin daurin watanni shida a gidan yari saboda samun su da laifin hada baki (ko tarar Naira 30,000 kowannensu), watanni uku kan aikata laifuka (ko tarar Naira 20,000 kowanne), shekara daya saboda zamba (ko kuma tarar Naira 20,000 kowanne), tarar Naira 30,000 kowanne), da watanni shida kan laifin karya cin amana (ko tarar Naira 20,000 kowanne).

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

Hukumar ta lura da cewa, duk da cewa babu wani korafi da tsohuwar ministar ya yi, an gano shirin nasu ne a yayin gudanar da bincike.

Hukumar ta kwato kudaden da aka damfara kuma za a mayar wa Aminu Dantata da Alhaji A.T. Gwarzo.

Dukkanin wadanda aka yankewa hukuncin kuma an bukaci su sanya hannu kan takardar yarjejeniya don su zamto masu kyawawan halaye.

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

EFCC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.