ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
EFCC

Hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta sanar da samun nasarar kama wasu mutum biyu da suka damfari wani dattijo Alhaji Aminu Dantata da tsohon minista Alhaji A.T. Gwarzo.

Bugu da kari, hukumar ta kwato Naira miliyan 5, daga hannun wadanda aka kama din sun damfari daga hannun hamshakin dan kasuwar, ciki har da Naira miliyan daya mallakin tsohon ministar bayan gurfanar da su gaban kotu.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala zaman kotun, lauyan masu shigar da kara Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bayyana cewa Bukar Galadima da Sulyman Ahmed sun shirya tare da aiwatar da wani shiri na damfarar wadanda abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

Bukar Galadima ya yi sojan gona da sunan Tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Abba Gana, inda nuna tsohon ministan ba shi da lafiya, ya kuma nemi taimakon Aminu Dantata, inda ya bukaci Naira miliyan 5 domin a yi masa magani, daga nan sai Dantata ya umarce shi da ya ba shi bayanan asusun ajiyarsa. A maimakon ya bayar da nasa, Galadima ya bayar da bayanan matarsa, Sadiyya Abba.

Daga nan ne dan kasuwar ya mika Naira miliyan 5 zuwa asusun ajiyar kudi domin tallafa wa wanda ke jinya.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

Daga baya, da Dantata ya tuntubi tsohon ministan don duba lafiyarsa, sai ya gane cewa an zambace shi, ya kai karar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, inda ta fara bincike.

An kama mutanen biyu ne kuma aka gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 24 da ke Kano.

Alkaliyar kotun ya yanke wa ’yan damfara hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru hudu a kowane makon da ya gabata.

An tuhumi mutanen biyu da laifin hada baki, damfara, cin amana, da kuma zamba.

Lokacin da aka karanta Rahoton Bayanin Farko, dukkansu sun amsa laifukan guda hudu. Lauyan masu gabatar da kara Barista Zahraddeen Hamisu Kofarmata ya bukaci a yi masa shari’a a karkashin sashe na 129 (8) na shari’ar ACJL 2019. Daga nan kuma aka yanke musu laifin.

Alkaliyar Kotun Majistare Umma Sani Kurawa ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin daurin watanni shida a gidan yari saboda samun su da laifin hada baki (ko tarar Naira 30,000 kowannensu), watanni uku kan aikata laifuka (ko tarar Naira 20,000 kowanne), shekara daya saboda zamba (ko kuma tarar Naira 20,000 kowanne), tarar Naira 30,000 kowanne), da watanni shida kan laifin karya cin amana (ko tarar Naira 20,000 kowanne).

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

Hukumar ta lura da cewa, duk da cewa babu wani korafi da tsohuwar ministar ya yi, an gano shirin nasu ne a yayin gudanar da bincike.

Hukumar ta kwato kudaden da aka damfara kuma za a mayar wa Aminu Dantata da Alhaji A.T. Gwarzo.

Dukkanin wadanda aka yankewa hukuncin kuma an bukaci su sanya hannu kan takardar yarjejeniya don su zamto masu kyawawan halaye.

Babban mai laifin da ke zaune a Kano, sai ya aika da Naira 500,000 ga wanda ya taimaka masa a Abuja, yayin da ya ajiye wa kansa Naira miliyan 4.5.

An kuma umarce su da su biya diyyar Naira miliyan 5 ko kuma su fuskanci daurin shekaru biyu a gidan yari bisa bukatar lauyan masu gabatar da kara.

Bugu da kari, masu laifin biyu sun yi amfani da irin wannan dabara wajen damfarar tsohon karamin ministan gidaje Alhaji A.T. Gwarzo na Naira miliyan daya.

EFCC
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Kantoman Yankin Musamman Na Macao Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.