ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kogi

Fadar shugaban kasa ta yi karin haske game da wasan kwaikwayo da rudanin shari’a da ke tattare da gazawar jami’an tsaro wajen cafke Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, duk da kokarin da aka yi.

Mai Magana Da Yawun Shugaban Kasar, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan yayin da yake magana a wani shirin zamantakewa da tattalin arziki na gidan talabijin na Channels, mai suna ‘Inside Sources with Laolu Akande’.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Onanuga ya bayyana kalubale na musamman da ke tattare da kusancin Bello da magajinsa, Gwamna Usman Ododo, wanda ke da kariyar tsarin mulki.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta tunatar da cewa, a watan Afrilu, Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta bayyana cewa ana neman Bello ne bisa zarginsa da aikata laifukan kudi da suka hada da Naira biliyan 80.2. Duk da cewa hukumar EFCC ta yi yunkurin cafke tsohon gwamnan, amma yunkurin ya ci tura, inda rahotanni suka ce Ododo ya kare Bello tare da ba wa gwamnan mafaka a masaukinsa.

Ya kara da cewa, yayin da hukumar EFCC ta dukufa wajen gurfanar da Bello a gaban kuliya, kariyar da aka bai wa Gwamna Ododo a karkashin tsarin mulki na dagula duk wani yunkuri na kama tsohon gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ita ce matsalar domin idan shi (Bello) ya zauna a gidan Gwamna Ododo, ‘yan sanda ba za su iya yin komai ba saboda za su keta wannan rigar da gwamna ke da ita.

“Kamar jami’in diflomasiyya ne da yake da kariya, don haka ba za ku iya yin komai game da shi ba. Kun tuna a Burtaniya lokacin da suke neman mutumin nan Wikileaks, sai ya je ya buya a wani ofishin jakadanci a Biritaniya, ba abin da su ( jami’an tsaro) za su iya yi, dole haka nan suka bar shi a can. Ina tsammanin daga baya ne ya fito suka kama shi,” Onanuga ya fadi haka yayin da yake tabbatar da rashin ikon EFCC.

Tsohon gwamnan Jihar Kogi, wanda ya yi mulki daga shekarar 2016 zuwa Mayu 2024, ya kasa gurfana a gaban kotu duk da yawan sammaci da kuma dage sauraren karar da aka yi masa.

Kogi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

June 6, 2026
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
Kotu Da Ɗansanda

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Next Post
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

LABARAI MASU NASABA

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad, Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad, Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.