• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta ƙasa (NDLEA), Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa mai ritaya ya bayyana dabarun da hukumar ta ke bi na kai hari kan kadarorin manyan masu dillalan kayan maye da masu safarar miyagun kwayoyi a wani taron manema labarai a Abuja.

Taron yana a matsayin wata alamar fara ayyukan da za a shafe mako guda don ranar yaƙin sha da fatauci kayan maye a Duniya na 2024. Marwa ya jaddada cewa kwace kadarorin wani muhimmin ɓangare ne na yaƙi da ayyukan miyagun kwayoyi da ruguza dabarsu.

  • Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa
  • Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

Marwa ya bayyana nasarar shirin hukumar NDLEA mai suna War Against Drug Abuse (WADA), wanda ke amfani da cikakkiyar tsarin rigakafin gurbacewar al’umma.

Ya jaddada cewa wannan shiri ne na bayar da shawarwari, da wayar da kan jama’a tare da karfafa haɗin gwuiwa a kan sha da fataucin muggan kwayoyi. Wannan ya yi dai-dai da taken ranar sha da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya ta shekarar 2024: “Shaida a bayyane take: Zuba Jari a Rigakafin,” wanda ke nuna muhimmancin matakan kariya don hana mutane yin ta’ammali da magunguna.

Da yake nuna godiya ga gwamnatin tarayya da ta jihohi da masu ruwa da tsaki daban-daban bisa goyon bayan da suka bayar, Marwa ya yi karin bayani kan ƙoƙarin haɗin gwuiwa da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa da suka hada da ofishin MDD kan yaƙi da miyagun kwayoyi (UNODC), hukumar yaƙi da fataucin miyagun kwayoyi ta Amurka (DEA), da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Mataimakin wakilin UNODC, Mista Danilo Campisi, ya buƙaci a ƙara bin duk matakan rigakafin domin daƙile hasashen ƙaruwar amfani da miyagun kwayoyi da kashi 40 cikin 100 nan da shekarar 2030, musamman a tsakanin matasa.

Taron ya jaddada muhimmancin ci gaba da inganta dabarun rigakafi shigowa da fara amfani muggan kwayoyi a cikin al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yau Kotun Tarayya Za Ta Yanke Hukuncin Masarautar Kano

Next Post

Jihar Kebbi Ta Yi Babbar Nasara A Aikin Hajjin Bana – Alhaji Faruk Yaro

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

58 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Jihar Kebbi Ta Yi Babbar Nasara A Aikin Hajjin Bana – Alhaji Faruk Yaro

Jihar Kebbi Ta Yi Babbar Nasara A Aikin Hajjin Bana – Alhaji Faruk Yaro

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.