Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Fara Shekarar Musulunci Daga Al-Muharram maimakon Rabi’ul Auwal

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Tambaya: Shin mene ne dalili da ya sa a ka fara kidayar shekarar Musulunci daga watan Muharram maimakon watan Rabi’ul Auwal, wanda  shi ne a ka yi hijira?

Amsa: An fara aiki da Shekarar Hijira ne bayan shudewar shekaru 17 da yin hijirar Sayyidina RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam), wato a zamanin halifancin Amirul-muminina Umar Bn al-Khaddab (Allah ya kara yarda da shi), inda a ka zabi watan al-Muharram ya zamo shi ne mafarin shekara, duk kuwa da cewa Sayyidina RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam) ya isa garin Madina a Hijirarsa ne a watan Rabi’ul Awwal.

Dalilin da ya sanya hankali sahabbai ya juyo wajen samar da matsaya game da tsarin kalanda kuwa shi ne, Sayyiduna Abu Musa Al-Ash’ariy (Allah ya kara yarda da shi) ne ya aika wa Sayyiduna Umar da sakon cewa, “Wasiku masu yawa su na zuwa ma na daga gare ka, amma babu kwanan wata.” Alal misali, sai a ce abu kaza ya faru a watan Sha’aban ba tare da an bambance watan Sha’aban na wace shekara ba.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Hakan ya sanya Sayyiduna Umar (Allah ya kara yarda da shi) ya tara sahabbai domin duba wannan al’amari. A lokacin ne wasu su ka ce mu fara shekarar Musulunci daga lokacin da a ka aiko Sayyiduna RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam), wasu kuma su ka ce ya kamata a fara ne daga lokacin hijirarsa (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam).

Sai Sayyiduna Umar (Allah ya kara yarda da shi) ya zabi a fara daga Hijira, ya na mai cewa, “Hijira ce ta bambance tsakanin gaskiya da karya.” Da haka a ka zabi Hijira ta zamo farkon shekarar Musulunci.

Game da zaben watan da za a fara shekarar da shi kuwa, shi ma an sami shawarwari mabambanta. Wasu su ka nuna a fara daga watan Ramadhan, ta yiwu saboda kasancewarsa watan da a ka saukar da Alkur’ani mai girma. Sai dai an zabi watan al-Muharram ne kasancewarsa lokacin da mutane su ke kama hanyarsu ta koma wa gida daga aikin Hajji

Wasu kuma su ka ce dalili zaben al-Muharram shi ne kasancewarsa watan da Sayyidina RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam) ya fara shirye-shiryen fita zuwa Hijira.

Al-Hafiz Ibn Hajar (Allah ya kara yarda da shi) ya bayyana cewa, an zaɓi wata al-Muharram ne a kan Rabi’ul Auwal, saboda a watan al-Muharram ne a ka fara azamar yin Hijira, domin mutanen Madina sun yi wa Sayyidina RasululLahi (SallalLahu alaiHi wa alihi wa sallam) mubaya’a ne a cikin watan Zul-Hajji. Wannan mubaya’ar ce ta share fage game da Hijira. Saboda haka sai a ka zabi al-Muharram.

Allah ne masani..

-An kwafo wannan ne daga Abdulkadir  Kurawa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Al’umman Bauchi Sun Fara Shaida Nagartarmu Cikin Kwanaki 100 – PDP

Next Post

Kogi 2019: Wakilai 2,578 Za Su Fiddo Dan Takarar PDP A Yau

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
7 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
8 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
20 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
1 day ago
0

...

Next Post
PDP Ta Ba Matawallen Maradun Tikitin Takarar Gwamnan Zamfara

Kogi 2019: Wakilai 2,578 Za Su Fiddo Dan Takarar PDP A Yau

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: