• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

by Abubakar Abba
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarinta na samar da mafita, ga ‘yan gudun hijira, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikinta na tallafa wa aikin aikin noma da ake kira ‘REHAEP’ ga ‘yan gudun hijirar da ke zaune a Jihar Filato, a sansaninsu na yankin Kpwasho a Karamar Hukumar Bassa ta jihar.

Har ila hau, aikin hadaka ne tsakanin hukumar kula da bakin haure da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa (NCFRMI) da kuma ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci.

  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu
  • Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

Kwamishinan hukumar, Tijjani Ahmed ya bayyana cewa; an ware gona mai fadin kadada 150, domin gudanar da wannan aiki, inda ya kara da cewa, ‘yan gudun hijira 300 za a tallafawa da kayan aiki da kuma tallafin kudi.

Haka zalika, Ahmed ya kara da cewa; su ma masana’antu masu zaman kansu, za su taimaka wajen tabbatar da ganin an yi girbin amfanin gonan da ‘yan gudun hijirar suka noma, wanda hakan zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Ya ci gaba da cewa, an wanzar da wannan aiki na gwaji a Jihohin Nasarawa da Borno, wanda kuma aka shirya fadada shi zuwa sauran jihohin kasar nan, har zuwa shekara biyar.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

A cewar Ahmed, za a shuka Irin noma kamar na Shinkafa, Masara, Dawa, Alkama da sauransu a cikin wadannan kadada 150.

Sanna kuma ya ce, ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, za ta samar da kayan aiki, domin noma hekta 150, inda kuma hukumar NCFRMI za ta samar da tallafin kudade ga ‘yan gudun hijirar.

Ahmed, wanda Darakata ne a hukumar; Fatima Mamman Daura ita ce ta wakilce shi tare da bayyana cewa, hukumar ta kuma yi hadaka da rundunar  tsaron farin kaya ta NSCDC da ke bai wa manoma kariya,

Shi kuwa gwamnan jihar, Caleb Muftwang a nasa jawabinn ya ce, ya kamata manoma a jihar su rika yin noma mai yawa, inda ya kara da cewa; gwamnatinsa za ta tallafa wa wadannan ‘yan gudun hijira.

Muftwang, wanda shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar ‘PLASSIMA’, Mista Sunday Audu ya wakilta a wajen taron ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa za ta tabbatar da an mayar da ‘yan gudun hijirar ga matsugunansu tare da magance kalubalen karatun ilimin boko na ‘ya’yansu.

A cewar tasa, a yanzu haka akawai hadakar da ake ci gaba da yi da jami’an tsaro da rundunar tsaron farin kaya ta NSCDC, domin karfafa tsaro a gonakan manoman ta yadda za su yi nomansu ba tare da jin wani tsoron harin ‘yan bindiga ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoNomaTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

Next Post

NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

7 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

7 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.