• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

by Abubakar Abba
1 year ago
Filato

A kokarinta na samar da mafita, ga ‘yan gudun hijira, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikinta na tallafa wa aikin aikin noma da ake kira ‘REHAEP’ ga ‘yan gudun hijirar da ke zaune a Jihar Filato, a sansaninsu na yankin Kpwasho a Karamar Hukumar Bassa ta jihar.

Har ila hau, aikin hadaka ne tsakanin hukumar kula da bakin haure da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa (NCFRMI) da kuma ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci.

  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu
  • Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

Kwamishinan hukumar, Tijjani Ahmed ya bayyana cewa; an ware gona mai fadin kadada 150, domin gudanar da wannan aiki, inda ya kara da cewa, ‘yan gudun hijira 300 za a tallafawa da kayan aiki da kuma tallafin kudi.

Haka zalika, Ahmed ya kara da cewa; su ma masana’antu masu zaman kansu, za su taimaka wajen tabbatar da ganin an yi girbin amfanin gonan da ‘yan gudun hijirar suka noma, wanda hakan zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Ya ci gaba da cewa, an wanzar da wannan aiki na gwaji a Jihohin Nasarawa da Borno, wanda kuma aka shirya fadada shi zuwa sauran jihohin kasar nan, har zuwa shekara biyar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

A cewar Ahmed, za a shuka Irin noma kamar na Shinkafa, Masara, Dawa, Alkama da sauransu a cikin wadannan kadada 150.

Sanna kuma ya ce, ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, za ta samar da kayan aiki, domin noma hekta 150, inda kuma hukumar NCFRMI za ta samar da tallafin kudade ga ‘yan gudun hijirar.

Ahmed, wanda Darakata ne a hukumar; Fatima Mamman Daura ita ce ta wakilce shi tare da bayyana cewa, hukumar ta kuma yi hadaka da rundunar  tsaron farin kaya ta NSCDC da ke bai wa manoma kariya,

Shi kuwa gwamnan jihar, Caleb Muftwang a nasa jawabinn ya ce, ya kamata manoma a jihar su rika yin noma mai yawa, inda ya kara da cewa; gwamnatinsa za ta tallafa wa wadannan ‘yan gudun hijira.

Muftwang, wanda shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar ‘PLASSIMA’, Mista Sunday Audu ya wakilta a wajen taron ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa za ta tabbatar da an mayar da ‘yan gudun hijirar ga matsugunansu tare da magance kalubalen karatun ilimin boko na ‘ya’yansu.

A cewar tasa, a yanzu haka akawai hadakar da ake ci gaba da yi da jami’an tsaro da rundunar tsaron farin kaya ta NSCDC, domin karfafa tsaro a gonakan manoman ta yadda za su yi nomansu ba tare da jin wani tsoron harin ‘yan bindiga ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.