• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

by Abubakar Abba
10 months ago
Jega

A ranar 9 ga watan Yulin 2024, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu; ya kaddamar da Kwamitin Fadar Shugaban Kasa, kan wanzar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi a Nijeriya.

Manufar ita ce, domin cimma burin farfado da fannin kiwo a fadin kasar baki-daya, wanda aka kiyasata samun akalla Naira tiriliyan 33, duba da yadda a fanin ke bayar da gudunmawa kasa da kashi uku cikin dari ga tattalin arzikin wannan kasa a duk shekara.

  • Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin
  • Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje

Kasancewar Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin guda cikin shugabanin kwamitin tare da wasu kwararrun mutane 23, Shugaban Kasa Tinubu kuma da kansa ne ke jagorantar kwamitin.

Kazalika, an kuma gindayawa kwamitin sharudda 16 na wanzar da sauye-sauye a fannin tare kuma da zamanantar da fannin na kiwo.

A rahoton farko, a bangaren rahoton Jega; ya bayar da wasu shawarwari, domin farfado da fannin; ciki har da kiwon don samun riba.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

A bangaren kiwon Kajin gidan gona, rahoton ya kiyasta tsintsayen da ake kiwo da suka kai kimanin miliyan 563, inda kwamtin ya shawarci gwamnatin tarayya da ta tallafa wa masu kiwon kajin gidan gonar su kimanin 185,000, da kayan aiki ga kanannan masu kiwon kajin gidan gona.

Kazalika, rahoton ya bayar da shawarar taimaka wa masu kiwon kaji kimanin 550,000; da sauran kungiyoyin da ke kiwon, wanda adadinsu ya kai 735,000.

Bugu da kari, rahoton ya kuma bayar da shawarar kula da saurin jinsin kajin cikin gidan da ake kiwatawa tare da samar da kayan aikin da ake adana naman da ake amfani da shi a cikin kasar.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kara habaka fannin kiwon kasar tare da kara karfafa kasuwancin fannin da suka hada da Cibiyar Bunkasa Binciken Kiwon Dabbobi da ke Garin Shika a Jihar Kaduna da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kirkiro da shirye-shiryen kiwon kajin gidan gona da samar da kayan zamani na gwajin lafiyar dabbobin tare kuma da samar da rijiyoyin burtsatsai da fitilu masu aiki da hasken rana a wuraren da masu kiwon kajin gidan gonan suke tare da samar da sassan kyankyasar kwan kajin gidan gona.

Kazakila, rahoton ya kuma bukaci a kara daga darajar kiwon kamar irin su Talo-talo, Agwagi, Tantabaru, Jimina da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa, yin amfani da wadannan shawarwari, za su taimaka wajen kara samun masu zuba hannun jari a fannin na kiwo a kasar.

Har ila yau, rahoton ya kuma bayar da shawara tare da kirkiro da cibiyar gudanar da bincike kan kiwon kajin gidan gona, wacce za ta ksanace daya daga cikin sabbi guda takwas na cibiyoyin gudanar da bincike.

Kazalika, rahoton ya shawarci gwamnatin da ta kara daga darajar cibiyar gudanar da binciken kiwon dabbobi ta kasa (NAPRI) tare kuma da kara daga darajar cibiyar gudanar da bincike, kan kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Cafke Matashin Da Ya Yi Lalata 'Yar Makocinsa Mai Shekara Takwas

LABARAI MASU NASABA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Jega

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.