• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

by Abubakar Abba
9 months ago
Jega

A ranar 9 ga watan Yulin 2024, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu; ya kaddamar da Kwamitin Fadar Shugaban Kasa, kan wanzar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi a Nijeriya.

Manufar ita ce, domin cimma burin farfado da fannin kiwo a fadin kasar baki-daya, wanda aka kiyasata samun akalla Naira tiriliyan 33, duba da yadda a fanin ke bayar da gudunmawa kasa da kashi uku cikin dari ga tattalin arzikin wannan kasa a duk shekara.

  • Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin
  • Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje

Kasancewar Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin guda cikin shugabanin kwamitin tare da wasu kwararrun mutane 23, Shugaban Kasa Tinubu kuma da kansa ne ke jagorantar kwamitin.

Kazalika, an kuma gindayawa kwamitin sharudda 16 na wanzar da sauye-sauye a fannin tare kuma da zamanantar da fannin na kiwo.

A rahoton farko, a bangaren rahoton Jega; ya bayar da wasu shawarwari, domin farfado da fannin; ciki har da kiwon don samun riba.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

A bangaren kiwon Kajin gidan gona, rahoton ya kiyasta tsintsayen da ake kiwo da suka kai kimanin miliyan 563, inda kwamtin ya shawarci gwamnatin tarayya da ta tallafa wa masu kiwon kajin gidan gonar su kimanin 185,000, da kayan aiki ga kanannan masu kiwon kajin gidan gona.

Kazalika, rahoton ya bayar da shawarar taimaka wa masu kiwon kaji kimanin 550,000; da sauran kungiyoyin da ke kiwon, wanda adadinsu ya kai 735,000.

Bugu da kari, rahoton ya kuma bayar da shawarar kula da saurin jinsin kajin cikin gidan da ake kiwatawa tare da samar da kayan aikin da ake adana naman da ake amfani da shi a cikin kasar.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kara habaka fannin kiwon kasar tare da kara karfafa kasuwancin fannin da suka hada da Cibiyar Bunkasa Binciken Kiwon Dabbobi da ke Garin Shika a Jihar Kaduna da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kirkiro da shirye-shiryen kiwon kajin gidan gona da samar da kayan zamani na gwajin lafiyar dabbobin tare kuma da samar da rijiyoyin burtsatsai da fitilu masu aiki da hasken rana a wuraren da masu kiwon kajin gidan gonan suke tare da samar da sassan kyankyasar kwan kajin gidan gona.

Kazakila, rahoton ya kuma bukaci a kara daga darajar kiwon kamar irin su Talo-talo, Agwagi, Tantabaru, Jimina da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa, yin amfani da wadannan shawarwari, za su taimaka wajen kara samun masu zuba hannun jari a fannin na kiwo a kasar.

Har ila yau, rahoton ya kuma bayar da shawara tare da kirkiro da cibiyar gudanar da bincike kan kiwon kajin gidan gona, wacce za ta ksanace daya daga cikin sabbi guda takwas na cibiyoyin gudanar da bincike.

Kazalika, rahoton ya shawarci gwamnatin da ta kara daga darajar cibiyar gudanar da binciken kiwon dabbobi ta kasa (NAPRI) tare kuma da kara daga darajar cibiyar gudanar da bincike, kan kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Cafke Matashin Da Ya Yi Lalata 'Yar Makocinsa Mai Shekara Takwas

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.