• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoma a jihohi daban-daban a kaar nan, na cikin fargabar aukuwar ambaliyar ruwan da za ta iya kwarara zuwa cikin gonakinsu.

Wasu daga cikin jihohin sun hada da Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu.

  • Kananan Manoma 31,666 Sun Samu Tallafin Noma Naira Biliyan 5.9 – CBN

Tuni dai, hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa ta sanar da cewa, ruwan da ya taru a Kogin Neja zai iya zama babbar barazana ga gonakan manoma, musamman wadanda ke jihohin Kebbi da Neja da Kwara da Nasarawa da Kogi da Anambra da Delta da Edo da Ribas da kuma Bayelsa wadanda kogin ya ke ta su.

Bugu da kari, Darakta-Janar na hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa, Mista Clement Onyeaso Nze a wani rahoton ta ya fitar, ya yi hasashen cewar za a fara samun ambaliya a kasar nan daga 6 ga watan Satumba a Jihar Kebbi.

Alalmisali, a daminar bara ambaliya ta jawo wa dubban manoma wadanda akasarinsu manoman shinkafa da masara ne a jihohin Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato, da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu, babbar asara.
Masana a fannin aikin noma a kasar nan, sun bayyana cewa, ambaliyar za ta jawo karancin abinci a a kasar nan, inda hakan zai kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Har ila yau, sakamakon ambaliyar ruwan da ta auku a daminar bara, ta jawo tashin farashin kayan abinci, misali, sai da farashin buhun masara a jihar Kano ya kai naira 20,000.

Bugu da kari, a jihar Binuwai kuwa, farashin ya kai naira 22,000; a birnin tarayar Abuja kuwa ya kai naira 24,000, inda a jihar Legas ta kai naira 25,000.

Lamarin na tashin farashin sakamokon aukuwar ta ambaliyar ruwa, sai da ya shafi farashin shinkafar da ake noma wa kasar nan, inda buhunta ya kai naira 55,000 a Abuja ya kai naira 58,000.

Wani masani a fanin samar da abinci ya sanar da cewa, kasar nan za ta iya aukawa a cikin matsalar karancin abinci.
Bugu da kari, a shekarar da ta gabata Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi ta sanar da cewa, sakamakon ambaliar da ta auku a bara, ta lalata kimain kadada 450,000 na gonakin shinkafa tare da lalata kadada 50,000.

Bisa hasashen da aka yi, manoma a jihar ta Kebbi sun tabka asarar da ta kai ta sama da naira biliyan biyar.
Wani manomin shinkafa a jihar ta Kebbi Garba Bala ya bayyana cewa, sakamakon ambaiyar ta bara ya yi asarar kimain kadada 16,000.

Ya kara da cewa, ya samo rancen ne daga banki don ya kara habaka nomansa na shinkafar wasu kuma daga cikin manoman shinkafar da iftila’in na ambaliyar ruwan ta aukawa gonakan su da suka shuka shinkafar sun bayyana cewa, samo rance ne a karkashin shirin aikin ma na gwamnatin tarayya na Anchor Borrowers da ke karkashin kulawar babban bankin Nijeriya.

Shi ma wani manomin shinkafa a jihar Sani Muhammad ya ce, ambaliayar ta lalata masa kadada shida tare da wasu kadada da ya shuka masara.

An ruwaito Shugaba kungiyar manoma ta kasa Ibrahim Kabiru ya ce ambaliyar ta fi shafar gonakin shinkafa da dawa da sauran amfanin gona.

Kabiru ya kara da cewa, zai yi wuya a iya iyakance barnar da ambaliya ta haifar a gonakan manoman, inda ya bayyana cewa, a gefe guda kuma manoma a kasar, musamman a arewacin kasar nan na ci gaba da fuskantar barazanar rashin tsaro saboda hare-haren ‘yan bindiga, inda hakan ya tilasta wa maona da dama, kaurace wa gonakinsu don gudun kar masu garkuwa su sace su ko kuma su hallaka su a yayin da suka je gonakarsu don yin noma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Next Post

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Related

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

4 hours ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

13 hours ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 days ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

7 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 week ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Next Post
Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

LABARAI MASU NASABA

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.