• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoma a jihohi daban-daban a kaar nan, na cikin fargabar aukuwar ambaliyar ruwan da za ta iya kwarara zuwa cikin gonakinsu.

Wasu daga cikin jihohin sun hada da Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu.

  • Kananan Manoma 31,666 Sun Samu Tallafin Noma Naira Biliyan 5.9 – CBN

Tuni dai, hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa ta sanar da cewa, ruwan da ya taru a Kogin Neja zai iya zama babbar barazana ga gonakan manoma, musamman wadanda ke jihohin Kebbi da Neja da Kwara da Nasarawa da Kogi da Anambra da Delta da Edo da Ribas da kuma Bayelsa wadanda kogin ya ke ta su.

Bugu da kari, Darakta-Janar na hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa, Mista Clement Onyeaso Nze a wani rahoton ta ya fitar, ya yi hasashen cewar za a fara samun ambaliya a kasar nan daga 6 ga watan Satumba a Jihar Kebbi.

Alalmisali, a daminar bara ambaliya ta jawo wa dubban manoma wadanda akasarinsu manoman shinkafa da masara ne a jihohin Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato, da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu, babbar asara.
Masana a fannin aikin noma a kasar nan, sun bayyana cewa, ambaliyar za ta jawo karancin abinci a a kasar nan, inda hakan zai kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Har ila yau, sakamakon ambaliyar ruwan da ta auku a daminar bara, ta jawo tashin farashin kayan abinci, misali, sai da farashin buhun masara a jihar Kano ya kai naira 20,000.

Bugu da kari, a jihar Binuwai kuwa, farashin ya kai naira 22,000; a birnin tarayar Abuja kuwa ya kai naira 24,000, inda a jihar Legas ta kai naira 25,000.

Lamarin na tashin farashin sakamokon aukuwar ta ambaliyar ruwa, sai da ya shafi farashin shinkafar da ake noma wa kasar nan, inda buhunta ya kai naira 55,000 a Abuja ya kai naira 58,000.

Wani masani a fanin samar da abinci ya sanar da cewa, kasar nan za ta iya aukawa a cikin matsalar karancin abinci.
Bugu da kari, a shekarar da ta gabata Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi ta sanar da cewa, sakamakon ambaliar da ta auku a bara, ta lalata kimain kadada 450,000 na gonakin shinkafa tare da lalata kadada 50,000.

Bisa hasashen da aka yi, manoma a jihar ta Kebbi sun tabka asarar da ta kai ta sama da naira biliyan biyar.
Wani manomin shinkafa a jihar ta Kebbi Garba Bala ya bayyana cewa, sakamakon ambaiyar ta bara ya yi asarar kimain kadada 16,000.

Ya kara da cewa, ya samo rancen ne daga banki don ya kara habaka nomansa na shinkafar wasu kuma daga cikin manoman shinkafar da iftila’in na ambaliyar ruwan ta aukawa gonakan su da suka shuka shinkafar sun bayyana cewa, samo rance ne a karkashin shirin aikin ma na gwamnatin tarayya na Anchor Borrowers da ke karkashin kulawar babban bankin Nijeriya.

Shi ma wani manomin shinkafa a jihar Sani Muhammad ya ce, ambaliayar ta lalata masa kadada shida tare da wasu kadada da ya shuka masara.

An ruwaito Shugaba kungiyar manoma ta kasa Ibrahim Kabiru ya ce ambaliyar ta fi shafar gonakin shinkafa da dawa da sauran amfanin gona.

Kabiru ya kara da cewa, zai yi wuya a iya iyakance barnar da ambaliya ta haifar a gonakan manoman, inda ya bayyana cewa, a gefe guda kuma manoma a kasar, musamman a arewacin kasar nan na ci gaba da fuskantar barazanar rashin tsaro saboda hare-haren ‘yan bindiga, inda hakan ya tilasta wa maona da dama, kaurace wa gonakinsu don gudun kar masu garkuwa su sace su ko kuma su hallaka su a yayin da suka je gonakarsu don yin noma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Next Post

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

20 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

1 day ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

LABARAI MASU NASABA

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.