ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa

by Abubakar Abba
4 years ago
Manoma

Manoma a jihohi daban-daban a kaar nan, na cikin fargabar aukuwar ambaliyar ruwan da za ta iya kwarara zuwa cikin gonakinsu.

Wasu daga cikin jihohin sun hada da Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu.

  • Kananan Manoma 31,666 Sun Samu Tallafin Noma Naira Biliyan 5.9 – CBN

Tuni dai, hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa ta sanar da cewa, ruwan da ya taru a Kogin Neja zai iya zama babbar barazana ga gonakan manoma, musamman wadanda ke jihohin Kebbi da Neja da Kwara da Nasarawa da Kogi da Anambra da Delta da Edo da Ribas da kuma Bayelsa wadanda kogin ya ke ta su.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, Darakta-Janar na hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa, Mista Clement Onyeaso Nze a wani rahoton ta ya fitar, ya yi hasashen cewar za a fara samun ambaliya a kasar nan daga 6 ga watan Satumba a Jihar Kebbi.

Alalmisali, a daminar bara ambaliya ta jawo wa dubban manoma wadanda akasarinsu manoman shinkafa da masara ne a jihohin Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato, da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu, babbar asara.
Masana a fannin aikin noma a kasar nan, sun bayyana cewa, ambaliyar za ta jawo karancin abinci a a kasar nan, inda hakan zai kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Har ila yau, sakamakon ambaliyar ruwan da ta auku a daminar bara, ta jawo tashin farashin kayan abinci, misali, sai da farashin buhun masara a jihar Kano ya kai naira 20,000.

Bugu da kari, a jihar Binuwai kuwa, farashin ya kai naira 22,000; a birnin tarayar Abuja kuwa ya kai naira 24,000, inda a jihar Legas ta kai naira 25,000.

Lamarin na tashin farashin sakamokon aukuwar ta ambaliyar ruwa, sai da ya shafi farashin shinkafar da ake noma wa kasar nan, inda buhunta ya kai naira 55,000 a Abuja ya kai naira 58,000.

Wani masani a fanin samar da abinci ya sanar da cewa, kasar nan za ta iya aukawa a cikin matsalar karancin abinci.
Bugu da kari, a shekarar da ta gabata Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi ta sanar da cewa, sakamakon ambaliar da ta auku a bara, ta lalata kimain kadada 450,000 na gonakin shinkafa tare da lalata kadada 50,000.

Bisa hasashen da aka yi, manoma a jihar ta Kebbi sun tabka asarar da ta kai ta sama da naira biliyan biyar.
Wani manomin shinkafa a jihar ta Kebbi Garba Bala ya bayyana cewa, sakamakon ambaiyar ta bara ya yi asarar kimain kadada 16,000.

Ya kara da cewa, ya samo rancen ne daga banki don ya kara habaka nomansa na shinkafar wasu kuma daga cikin manoman shinkafar da iftila’in na ambaliyar ruwan ta aukawa gonakan su da suka shuka shinkafar sun bayyana cewa, samo rance ne a karkashin shirin aikin ma na gwamnatin tarayya na Anchor Borrowers da ke karkashin kulawar babban bankin Nijeriya.

Shi ma wani manomin shinkafa a jihar Sani Muhammad ya ce, ambaliayar ta lalata masa kadada shida tare da wasu kadada da ya shuka masara.

An ruwaito Shugaba kungiyar manoma ta kasa Ibrahim Kabiru ya ce ambaliyar ta fi shafar gonakin shinkafa da dawa da sauran amfanin gona.

Kabiru ya kara da cewa, zai yi wuya a iya iyakance barnar da ambaliya ta haifar a gonakan manoman, inda ya bayyana cewa, a gefe guda kuma manoma a kasar, musamman a arewacin kasar nan na ci gaba da fuskantar barazanar rashin tsaro saboda hare-haren ‘yan bindiga, inda hakan ya tilasta wa maona da dama, kaurace wa gonakinsu don gudun kar masu garkuwa su sace su ko kuma su hallaka su a yayin da suka je gonakarsu don yin noma.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.