• English
  • Business News
Monday, June 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsuntsaye Jan-baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da daminar bana ta kankama sosai, wasu manoma da ke kasar nan, musamman a Arewacin kasar sun fara fargabar bullar tsuntsaye masu jan-baki wadanda ke lalata amfanin gonakinsu.

Bugu da kari, fargabar ta manoman ta zo ne lokacin da a kasar nan ake ci gaba da fuskanatar karancin abinci, musamman ganin yadda ‘yan bindiga suka hana yawancin manoman da ke fadin kasar nan, musamman na karkara zuwa gonakinsu domin nomansu.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni

A bara, wasu daga cikin kauyukana da wannnan annobar ta tsintsayen ta auka wa sun hada da, Tudun-Mai-Tandu da ke cikin karamar hukumar Dange Shuni a jihar Sakkwato, inda rahotanni suka tabbatar da cewa, irin wadannan tsintsayen sun yi wa gonakin manoman da ke kauyen kawanya, suka kuma lalata musu amfanin gonakinsu.

Ko a bara Shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar Sakkwato, Alhaji Sambo Abubakar ya bayyana cewa, tsuntsaye sun shiga gonakisnu, inda suka lalala musu Shinkafar da suka shuka.

A cewarsa,sakamakon shigar da tsuntsayen suka yi cikin gonakinsu, sun yi asara mai yawa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

In za a iya tuna wa, a bara, gwamnatin tarayyar ta shelanta cewa, ta ware naira biliyan goma sha uku da miliyan dari, musamman domin ta yaki halittun da ke illata amfanin gona, bayan an yi shuka.

A cewar gwamnatin, a cikin wadanan kudaden har da wadanda za a tallafa da su wajen dakile shigowar tsuntsayen cikin kasar nan, musamman a jihohin arewa.

Wasu daga cikin manoman, irin su, Malam Umaru Garba Shuni, wanda yana daya daga cikin maomnan da tsutsayen suka auka cikin gonarsa, ya sanar da cewa, tsuntsayen sun yi wa amfanin gona da ya shuka illa.

A cewar Malam Umaru, tsuntsayen sun shiga gonarsa, inda suka lalata masa amfani.
Shi ma wani manomi a kauyen, mai suna Alhaji Sambo, ya nuna cewa, kafin gwamnati ta kawo musu dauki wasu manoma a kauyen, na amfani da wani salo na gargajiya wajen korar tsuntsayen.
Alhaji Sambo ya ci gaba da cewa, lokacin da tsitsayen suka bulla gonanarsu sun yi kokarin korarsu daga cikin gonakinsu, inda ya kara da cewa, amma idan har tsuntsayen suka ji karar wasu abubuwan da manoman suke kada wa don su kore su daga cikin gonakinsu sai su gudu, haka kuma, suna yin amfani da zaren kaset na bidiyo wanda idan iska ta kada, sai tsuntsayem su fice daga cikin gonakin nasu.

Haka kuma, shi ma wani manomin mai suna Malam Murtala Gagadu ya bayyana cewa,a bara, tsuntsayen sun bulla a wasu yankunan Isa, da Sabon-birni, da Wurno, da Wammako.

Ya kara da cewa, hakan sai ya sa suka bukaci agaji daga hukumomin aiki gona a jihar da kuma tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

Next Post

Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

1 day ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

2 days ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Inabi

Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.