• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsuntsaye Jan-baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da daminar bana ta kankama sosai, wasu manoma da ke kasar nan, musamman a Arewacin kasar sun fara fargabar bullar tsuntsaye masu jan-baki wadanda ke lalata amfanin gonakinsu.

Bugu da kari, fargabar ta manoman ta zo ne lokacin da a kasar nan ake ci gaba da fuskanatar karancin abinci, musamman ganin yadda ‘yan bindiga suka hana yawancin manoman da ke fadin kasar nan, musamman na karkara zuwa gonakinsu domin nomansu.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni

A bara, wasu daga cikin kauyukana da wannnan annobar ta tsintsayen ta auka wa sun hada da, Tudun-Mai-Tandu da ke cikin karamar hukumar Dange Shuni a jihar Sakkwato, inda rahotanni suka tabbatar da cewa, irin wadannan tsintsayen sun yi wa gonakin manoman da ke kauyen kawanya, suka kuma lalata musu amfanin gonakinsu.

Ko a bara Shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar Sakkwato, Alhaji Sambo Abubakar ya bayyana cewa, tsuntsaye sun shiga gonakisnu, inda suka lalala musu Shinkafar da suka shuka.

A cewarsa,sakamakon shigar da tsuntsayen suka yi cikin gonakinsu, sun yi asara mai yawa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

In za a iya tuna wa, a bara, gwamnatin tarayyar ta shelanta cewa, ta ware naira biliyan goma sha uku da miliyan dari, musamman domin ta yaki halittun da ke illata amfanin gona, bayan an yi shuka.

A cewar gwamnatin, a cikin wadanan kudaden har da wadanda za a tallafa da su wajen dakile shigowar tsuntsayen cikin kasar nan, musamman a jihohin arewa.

Wasu daga cikin manoman, irin su, Malam Umaru Garba Shuni, wanda yana daya daga cikin maomnan da tsutsayen suka auka cikin gonarsa, ya sanar da cewa, tsuntsayen sun yi wa amfanin gona da ya shuka illa.

A cewar Malam Umaru, tsuntsayen sun shiga gonarsa, inda suka lalata masa amfani.
Shi ma wani manomi a kauyen, mai suna Alhaji Sambo, ya nuna cewa, kafin gwamnati ta kawo musu dauki wasu manoma a kauyen, na amfani da wani salo na gargajiya wajen korar tsuntsayen.
Alhaji Sambo ya ci gaba da cewa, lokacin da tsitsayen suka bulla gonanarsu sun yi kokarin korarsu daga cikin gonakinsu, inda ya kara da cewa, amma idan har tsuntsayen suka ji karar wasu abubuwan da manoman suke kada wa don su kore su daga cikin gonakinsu sai su gudu, haka kuma, suna yin amfani da zaren kaset na bidiyo wanda idan iska ta kada, sai tsuntsayem su fice daga cikin gonakin nasu.

Haka kuma, shi ma wani manomin mai suna Malam Murtala Gagadu ya bayyana cewa,a bara, tsuntsayen sun bulla a wasu yankunan Isa, da Sabon-birni, da Wurno, da Wammako.

Ya kara da cewa, hakan sai ya sa suka bukaci agaji daga hukumomin aiki gona a jihar da kuma tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

Next Post

Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

1 day ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

2 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

2 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

3 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

1 week ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

1 week ago
Next Post
Inabi

Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.