ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

by Abubakar Abba
4 years ago
Tsuntsaye Jan-baki

A yayin da daminar bana ta kankama sosai, wasu manoma da ke kasar nan, musamman a Arewacin kasar sun fara fargabar bullar tsuntsaye masu jan-baki wadanda ke lalata amfanin gonakinsu.

Bugu da kari, fargabar ta manoman ta zo ne lokacin da a kasar nan ake ci gaba da fuskanatar karancin abinci, musamman ganin yadda ‘yan bindiga suka hana yawancin manoman da ke fadin kasar nan, musamman na karkara zuwa gonakinsu domin nomansu.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni

A bara, wasu daga cikin kauyukana da wannnan annobar ta tsintsayen ta auka wa sun hada da, Tudun-Mai-Tandu da ke cikin karamar hukumar Dange Shuni a jihar Sakkwato, inda rahotanni suka tabbatar da cewa, irin wadannan tsintsayen sun yi wa gonakin manoman da ke kauyen kawanya, suka kuma lalata musu amfanin gonakinsu.

ADVERTISEMENT

Ko a bara Shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar Sakkwato, Alhaji Sambo Abubakar ya bayyana cewa, tsuntsaye sun shiga gonakisnu, inda suka lalala musu Shinkafar da suka shuka.

A cewarsa,sakamakon shigar da tsuntsayen suka yi cikin gonakinsu, sun yi asara mai yawa.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

In za a iya tuna wa, a bara, gwamnatin tarayyar ta shelanta cewa, ta ware naira biliyan goma sha uku da miliyan dari, musamman domin ta yaki halittun da ke illata amfanin gona, bayan an yi shuka.

A cewar gwamnatin, a cikin wadanan kudaden har da wadanda za a tallafa da su wajen dakile shigowar tsuntsayen cikin kasar nan, musamman a jihohin arewa.

Wasu daga cikin manoman, irin su, Malam Umaru Garba Shuni, wanda yana daya daga cikin maomnan da tsutsayen suka auka cikin gonarsa, ya sanar da cewa, tsuntsayen sun yi wa amfanin gona da ya shuka illa.

A cewar Malam Umaru, tsuntsayen sun shiga gonarsa, inda suka lalata masa amfani.
Shi ma wani manomi a kauyen, mai suna Alhaji Sambo, ya nuna cewa, kafin gwamnati ta kawo musu dauki wasu manoma a kauyen, na amfani da wani salo na gargajiya wajen korar tsuntsayen.
Alhaji Sambo ya ci gaba da cewa, lokacin da tsitsayen suka bulla gonanarsu sun yi kokarin korarsu daga cikin gonakinsu, inda ya kara da cewa, amma idan har tsuntsayen suka ji karar wasu abubuwan da manoman suke kada wa don su kore su daga cikin gonakinsu sai su gudu, haka kuma, suna yin amfani da zaren kaset na bidiyo wanda idan iska ta kada, sai tsuntsayem su fice daga cikin gonakin nasu.

Haka kuma, shi ma wani manomin mai suna Malam Murtala Gagadu ya bayyana cewa,a bara, tsuntsayen sun bulla a wasu yankunan Isa, da Sabon-birni, da Wurno, da Wammako.

Ya kara da cewa, hakan sai ya sa suka bukaci agaji daga hukumomin aiki gona a jihar da kuma tarayya.

Tsuntsaye Jan-baki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Inabi

Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.