ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

by Abubakar Abba
4 years ago
Tsuntsaye Jan-baki

A yayin da daminar bana ta kankama sosai, wasu manoma da ke kasar nan, musamman a Arewacin kasar sun fara fargabar bullar tsuntsaye masu jan-baki wadanda ke lalata amfanin gonakinsu.

Bugu da kari, fargabar ta manoman ta zo ne lokacin da a kasar nan ake ci gaba da fuskanatar karancin abinci, musamman ganin yadda ‘yan bindiga suka hana yawancin manoman da ke fadin kasar nan, musamman na karkara zuwa gonakinsu domin nomansu.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni

A bara, wasu daga cikin kauyukana da wannnan annobar ta tsintsayen ta auka wa sun hada da, Tudun-Mai-Tandu da ke cikin karamar hukumar Dange Shuni a jihar Sakkwato, inda rahotanni suka tabbatar da cewa, irin wadannan tsintsayen sun yi wa gonakin manoman da ke kauyen kawanya, suka kuma lalata musu amfanin gonakinsu.

ADVERTISEMENT

Ko a bara Shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar Sakkwato, Alhaji Sambo Abubakar ya bayyana cewa, tsuntsaye sun shiga gonakisnu, inda suka lalala musu Shinkafar da suka shuka.

A cewarsa,sakamakon shigar da tsuntsayen suka yi cikin gonakinsu, sun yi asara mai yawa.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

In za a iya tuna wa, a bara, gwamnatin tarayyar ta shelanta cewa, ta ware naira biliyan goma sha uku da miliyan dari, musamman domin ta yaki halittun da ke illata amfanin gona, bayan an yi shuka.

A cewar gwamnatin, a cikin wadanan kudaden har da wadanda za a tallafa da su wajen dakile shigowar tsuntsayen cikin kasar nan, musamman a jihohin arewa.

Wasu daga cikin manoman, irin su, Malam Umaru Garba Shuni, wanda yana daya daga cikin maomnan da tsutsayen suka auka cikin gonarsa, ya sanar da cewa, tsuntsayen sun yi wa amfanin gona da ya shuka illa.

A cewar Malam Umaru, tsuntsayen sun shiga gonarsa, inda suka lalata masa amfani.
Shi ma wani manomi a kauyen, mai suna Alhaji Sambo, ya nuna cewa, kafin gwamnati ta kawo musu dauki wasu manoma a kauyen, na amfani da wani salo na gargajiya wajen korar tsuntsayen.
Alhaji Sambo ya ci gaba da cewa, lokacin da tsitsayen suka bulla gonanarsu sun yi kokarin korarsu daga cikin gonakinsu, inda ya kara da cewa, amma idan har tsuntsayen suka ji karar wasu abubuwan da manoman suke kada wa don su kore su daga cikin gonakinsu sai su gudu, haka kuma, suna yin amfani da zaren kaset na bidiyo wanda idan iska ta kada, sai tsuntsayem su fice daga cikin gonakin nasu.

Haka kuma, shi ma wani manomin mai suna Malam Murtala Gagadu ya bayyana cewa,a bara, tsuntsayen sun bulla a wasu yankunan Isa, da Sabon-birni, da Wurno, da Wammako.

Ya kara da cewa, hakan sai ya sa suka bukaci agaji daga hukumomin aiki gona a jihar da kuma tarayya.

Tsuntsaye Jan-baki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Inabi

Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.