• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Kasar Zimbabwe Ya Aure Mahaifiyarsa Bayan Ya Yi Mata Ciki

by Leadership Hausa
1 year ago
Aure

Wata uwa ‘yar kasar Zimbabwe da danta sun yi ikirarin cewa suna soyayya da juna kuma sun yanke shawarar su yi aure bisa la’akari da cewa mahaifiyar Betty Mbereko (daga Mwenezi a Masbingo) tana da ciki wata shida a yanzu kuma tana jiran haihuwar abin da ke cikinta wanda zai zama danta kuma jikanta.

Mbereko, mai shekaru 40, ta kasance bazawara tun shekaru 12 da suka gabata inda take zaune da danta mai shekaru 23 mai suna Farai Mbereko.

  • Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano
  • Harajin Da EU Ta Sanyawa Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin, Ita Zai Yi Wa Illa

Ta tabbatar da cewa tana da ciki wata shida kuma ta yanke shawarar cewa zai fi kyau ta “aure” danta domin ba ta son auren ’yan’uwan mijinta da ya rasu, wadanda ta ce suna matukar kwadayin ganin sun aure ta.

Betty ta girgiza wata kotun akuye a makon da ya gabata lokacin da ta ce ta fara kaunar dan nata ne a matsayin wanda za ta iya aura tun shekaru uku da suka wuce. Ta ce bayan kashe makudan kudade ta tura Farai makaranta bayan rasuwar mijinta, don haka ta ji cewa tana da hakki a kan kudin da yake samu yanzu domin babu wata mace da ta cancanci hakan.

“Duba da cewa, ni kadai na yi ta fama da gwagwarmaya don in tura dana makaranta, ba wanda ya taimake ni. Yanzu ka ga dana yana aiki kuma don na ce zan aure shi sai ka zarge ni da aikata ba daidai ba?

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

“A bar ni kawai in ji dadin gumina da na barje,” ta fada wa kotun kauyen.

A nashi bangaren, dan nata, Farai ya ce shi kansa ya fi son ya aure mahaifiyarsa kuma zai biya ragowar bashin sadakin da mahaifinsa ya gadar wa a kakanninsa.

“Na san mahaifina ya rasu kafin ya gama biyan kudin sadaki kuma a shirye nake in biya,” in ji shi.

“Yana da kyau a bayyana abin da ke faruwa domin mutane su sani cewa ni ne na yi wa mahaifiyata ciki. Idan ba haka ba, za su tuhume ta da fasikanci.”

Sai dai kuma, Dagacin kauyen, Nathan Muputirwa ya ce: “Ba za mu kyale hakan ya faru a kauyenmu ba, domin hakika wannan mummunan al’amari ne). Idan da a zamanin baya suka yi hakan dole ne a zartar musu da hukuncin kisa amma a yau ba za mu iya ba saboda muna tsoron ‘yansanda.”

Ya gargade su da su gaggauta yanke wannan kudiri na auren junansu ko kuma su bar kauyen da zama.

Tuni dai majiyarmu ta bayyana cewa uwar da dan sun zabi su yi hijira daga kauyen inda suka koma wani wuri da ba a bayyana ba.

Majiya: One Africa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Next Post
Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza – Majalisar Dinkin Duniya

Isra’ila Na Ci Gaba Da Take Dokokin Duniya A Gaza - Majalisar Dinkin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.