• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Majalisar Tarayya Na PDP A Kano Municipal, Da’awah Ya Rabawa Dalibai 500 JAMB

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Dalibai 500 'Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da'awah

Dalibai 500 'Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da'awah

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar majalisar tarayya na Jam’iyyar PDP a karamar hukumar birni, Hon. Injiniya Yusuf Abdullahi Da’awah, ya gwangwaje dalibai 500 ‘Yan asalin Kano Municipal da rabon Jarabawar shiga makarantun gaba da sinkandire ta UTME wacce aka fi sani da JAMB.

Hon. Yusuf Abdullahi Da'awah
Hon. Yusuf Abdullahi Da’awah

An gudanar da taron rabon jarabawar a yammacin ranar Asabar din nan 18, ga Febarairun 2023 a filin taro na kofar gidan Qadiriyya da ke unguwar Kabara mazabar Tudun Wuzirchi a karamar hukumar birni.

  • Da’awa Ya Kaddamar Da Shirin Mayar Da Yara 1300 Makaranta Da Rabon Kayan Karatu
  • Atiku Ya Kaddamar Da Makarantar Haddar Al-Kur’ani A Kano

A jawabinsa a wurin taron, Injiniya Da’awah, ya godewa Allah bisa wannan dama da ya samu ta daukar nauyin ba wa dalibai 500 JAMB a karo na bakwai bayan rabon Jarabawar NECO da aka yi a baya da rabon kayan makaranta ga ‘Yan Firamare da litittafai da jaka.

Dalibai 500 'Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da'awah
Dalibai 500 ‘Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da’awah

Da’awah ya yi wa daliban alkawarin cewa matsawar ya yi nasara a zaben da za a gudanar ranar asabar mai zuwa 25, ga Febarairun 2023 zai dauki nauyin karatunsu har su kammala karatu a Jami’o’in da suka samu gurbin karatu tare da samar musu da aikin yi bayan sun kammala karatun.

Dalibai 500 Da Suka Ci Gajiyar Tallafin JAMB Daga Hon Da'awah Lokacin Da Suke Karbar Horo Kan Jarabawar
Dalibai 500 Lokacin Da Suke Karbar Horo Kan Jarabawar JAMB

Da’awah ya ce, rabon jarabawar ba siyasa a ciki don kuwa babu wanda ya sani cikin daliban, an yada sanarwar ne kawai ta kafafen sada zumunta, su kuma daliban sun cike aka kuma dauke su bisa cancantarsu.

Labarai Masu Nasaba

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Yusuf Da’awah ya yi alkawarin daukar nauyin yi wa daliban horo kan yadda za su rubuta jarabawar ta JAMB, ya kuma bukaci sauran Jama’a da su yi koyi da wannan tsarin don tallafar ‘ya’yan talakawa.

A nasu jawabin a wurin taron, wasu cikin daliban da suka ci gajiyar shirin, Umar Muhammad da Zainab Hassan Yahaya, sun godewa Da’awah bisa kokarinsa na bayar da tallafin karatun ga dalibai marasa karfi da addu’ar Allah ya kara daga darajarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuDa'awahJambkanoKano MunicipalPDPRabon JAMBUTME
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoman Jihar Inugu Sun Bukaci Gwamnatin Ta Tallafa Musu Da Rance

Next Post

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

Related

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

27 minutes ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

1 hour ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

2 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

16 hours ago
Next Post
Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

LABARAI MASU NASABA

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.