• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Majalisar Tarayya Na PDP A Kano Municipal, Da’awah Ya Rabawa Dalibai 500 JAMB

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Dalibai 500 'Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da'awah

Dalibai 500 'Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da'awah

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar majalisar tarayya na Jam’iyyar PDP a karamar hukumar birni, Hon. Injiniya Yusuf Abdullahi Da’awah, ya gwangwaje dalibai 500 ‘Yan asalin Kano Municipal da rabon Jarabawar shiga makarantun gaba da sinkandire ta UTME wacce aka fi sani da JAMB.

Hon. Yusuf Abdullahi Da'awah
Hon. Yusuf Abdullahi Da’awah

An gudanar da taron rabon jarabawar a yammacin ranar Asabar din nan 18, ga Febarairun 2023 a filin taro na kofar gidan Qadiriyya da ke unguwar Kabara mazabar Tudun Wuzirchi a karamar hukumar birni.

  • Da’awa Ya Kaddamar Da Shirin Mayar Da Yara 1300 Makaranta Da Rabon Kayan Karatu
  • Atiku Ya Kaddamar Da Makarantar Haddar Al-Kur’ani A Kano

A jawabinsa a wurin taron, Injiniya Da’awah, ya godewa Allah bisa wannan dama da ya samu ta daukar nauyin ba wa dalibai 500 JAMB a karo na bakwai bayan rabon Jarabawar NECO da aka yi a baya da rabon kayan makaranta ga ‘Yan Firamare da litittafai da jaka.

Dalibai 500 'Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da'awah
Dalibai 500 ‘Yan Asalin Kano Municipal Da Suka Ci Gajiyar Tallafin Jarabawar JAMB Daga Hon Da’awah

Da’awah ya yi wa daliban alkawarin cewa matsawar ya yi nasara a zaben da za a gudanar ranar asabar mai zuwa 25, ga Febarairun 2023 zai dauki nauyin karatunsu har su kammala karatu a Jami’o’in da suka samu gurbin karatu tare da samar musu da aikin yi bayan sun kammala karatun.

Dalibai 500 Da Suka Ci Gajiyar Tallafin JAMB Daga Hon Da'awah Lokacin Da Suke Karbar Horo Kan Jarabawar
Dalibai 500 Lokacin Da Suke Karbar Horo Kan Jarabawar JAMB

Da’awah ya ce, rabon jarabawar ba siyasa a ciki don kuwa babu wanda ya sani cikin daliban, an yada sanarwar ne kawai ta kafafen sada zumunta, su kuma daliban sun cike aka kuma dauke su bisa cancantarsu.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Yusuf Da’awah ya yi alkawarin daukar nauyin yi wa daliban horo kan yadda za su rubuta jarabawar ta JAMB, ya kuma bukaci sauran Jama’a da su yi koyi da wannan tsarin don tallafar ‘ya’yan talakawa.

A nasu jawabin a wurin taron, wasu cikin daliban da suka ci gajiyar shirin, Umar Muhammad da Zainab Hassan Yahaya, sun godewa Da’awah bisa kokarinsa na bayar da tallafin karatun ga dalibai marasa karfi da addu’ar Allah ya kara daga darajarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuDa'awahJambkanoKano MunicipalPDPRabon JAMBUTME
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoman Jihar Inugu Sun Bukaci Gwamnatin Ta Tallafa Musu Da Rance

Next Post

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

7 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

10 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

12 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

14 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

15 hours ago
Next Post
Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

Ta Yaya Aka Samu Nasarar Kiyaye Rayuka Da Lafiyar Al’ummar Sinawa Daga Cutar COVID-19?

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.