• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da’awa Ya Kaddamar Da Shirin Mayar Da Yara 1300 Makaranta Da Rabon Kayan Karatu

by Muhammad
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Da’awa Ya Kaddamar Da Shirin Mayar Da Yara 1300 Makaranta Da Rabon Kayan Karatu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar Majalisar Tarayya a Jam’iyyar PDP a Kano Municipal, Yusuf Da’awa, ya kaddamar da taron sanya yara marasa galihu guda 1300 a makaranta da samar musu da kayan makaranta da sauran ababan koyon karatu.

Wani sashe na yaran da suka amfana da tallafin karatu na Yusuf Da’awa.

Injiniya Da’awa, ya ce manufar bayar da tallafin shi ne samar da karin masu zuwa makaranta ga yaran da iyayensu ba su da karfin daukar nauyin karatunsu.

  • 2023: Sarkin Kano Da Kungiyoyin Fararen Hula Sun Bukaci INEC Ta Gudanar Da Sahihin Zabe 
  • Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano – Kwamishina

A cewar Da’awa, “babu yadda za a magance tarin matsalolin da ke damun al’umarmu ba tare da an samar da wata dama da yara zasu samu ilimi ba, ba tare da la’akari da nauyin aljihun iyayensu ba.”

Da’awa yayin rabon kayan karatu ga Yara 1300 a mazabar Kano Municipal.

“Allah ya sani ni dan talakawa ne kuma ina alfahari da damar da Allah ya bani ta taimakawa al’uma, kuma babban buri na shi ne yadda muka hadu anan a ce bayan wasu shekaru an samu wasu daga cikin wadannan yara sun tara wasu yayan talakawa domin daukar nauyin karatunsu, ko da rai na ko babu.”

Daga nan Injiniya Yusuf Abdullahi, wanda shi ne mafi kankantar shekaru cikin jerin ‘yan takara masu neman sahalewar al’umarsu domin su wakilce su a majalisar wakilai ta tarayyar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“A baya mun dauki nauyin karatun dalibai da dama wajen rubuta jarabawar WAEC da NECO da kuma JAMB tsahon shekaru da suka wuce,”

“Hakan kuwa na da nasaba da nazari da muka yi akan alkaluma da ke nuni da cewa wani kaso mafi tsoka na dalibai kan hakura da ci gaba da karatu saboda gazawa wajen samun kudin wadannan jarabawa, shi yasa muka dukufa wajen ganin cewa mun yi iya yinmu wajen tabbatar da cewa mun tallafi karatun dalibai da dama a fadin wannan karamar hukuma.” Cewar Da’awa.

Da’awa ya kuma kara da cewa nan gaba kadan zai sake kaddamar da shirin koyar da sana’o’in dogaro da kai ga mata da matasa, domin rage radadin tattalin arziki da ake fama da shi.

Daga cikin manyan bakin da suka halarci taron, akwai tsohon kakakin majalisar wakilai ta kasa, Ghali Umar Na’abba da jigo a jam’iyyar PDP a nan Kano, Ibrahim Aminu Dan’iya da ma sauran manyan masu ruwa da tsaki na karamar hukumar birni da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sake Zaben Sin A Matsayin Mambar Hukumar ITU

Next Post

Chen Xu:Ya Kamata A Bincika Tare Da Daukar Matakan Doka Kan Wandanda Suke Keta Hakkokin Yara ’Yan Asalin Afirka

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Chen Xu:Ya Kamata A Bincika Tare Da Daukar Matakan Doka Kan Wandanda Suke Keta Hakkokin Yara ’Yan Asalin Afirka

Chen Xu:Ya Kamata A Bincika Tare Da Daukar Matakan Doka Kan Wandanda Suke Keta Hakkokin Yara ’Yan Asalin Afirka

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.