Aliko Dangote ya yi murabus daga shugabancin kamfanin siminti, wanda ya kafa kuma ya gina ya zama mafi girma a nahiyar Afirka.
Ya ajiye muƙamin ne domin ya mayar da hankali kan aikin matatarsa ta man fetur, masana’antar sinadaran roba da taki, da kuma hulɗarsa da gwamnati.
- 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
- Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
An naɗa Emmanuel Ikazoboh, ɗaya daga cikin mambobin hukumar gudanarwar kamfanin, a matsayin sabon Shugaban kamfanin.
Hajiya Mariya Aliko Dangote ta shiga cikin hukumar gudanarwar kamfanin, bayan ritayar Farfesa Dorothy Ufot.
A lokacin shugabancin Dangote, kamfanin ya samu riba mai yawa, ya ƙara yawan fitar da kaya zuwa ƙasashen waje, tare da faɗaɗa ayyukansa a sassa daban-daban na Afirka.
Ikazoboh, ya ce ya jin daɗin samun wannan dama, kuma zai yi aiki tuƙuru don rage farashi da kuma amfani da makamashi mai tsafta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp