• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

by Sulaiman Bala Idris
8 months ago
in Ra'ayoyi
0
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wata ziyarar aiki da na yi a tsakiyar watan Agusta, direbana a Jihar Taraba ya shafe kusan fiye da rabin tafiyar zuwa masaukin mu yana magana a kan Gwamnan Zamfara, wanda kuma shi ne mai gidana.

Direban ya ambaci cewa gwamnan shi ne mafi karancin shekaru a cikin gwamnoni, mutum na musamman, wanda kuma kuma bai gajiya da aiki. Na tasa kunne ina saurare saboda mun saba jin irin wadannan dadadan maganganu game da Dauda Lawal.

  • Gwamnatin Katsina Ta Sassauta Dokar Hana Yawon Dare A FaÉ—in Jihar
  • Gwamna Dauda Ya Ziyarci Yankunan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Gummi

A yau, 2 ga Satumba, 2024, mai gidana, wanda a kodayaushe ake yawan ganinsa a matsayin matashi, yana cika shekara 59 a duniya. Tun a makon da ya gabata nake ta zurfafa tunani kan abin da zan rubuta a matsayin karramawa ga Gwamna Dauda Lawal. A baya na yi rubutu da yawa a irin wannan rana, amma wadanda na fi so a zuciyata fiye da kowanne su ne masu taken ‘Dauda Lawal: Mutuminmu, Burin Al’umma’ da ‘Dauda Lawal Din Da Na Sani’.

A ranar 29 ga Mayu, 2023, wani sabon babi ya bude a rayuwarmu yayin da Dauda Lawal, mutumin da muka sani a matsayin mai zaman kansa, ya karbi kujerar gwamnan jha. A yanzu ya dauki nauyin mulkin jihar da ke fama da matsalar ’yan bindiga, koma-baya a bangaren harkokin ilimi, kiwon lafiya, da walwalar ma’aikatan gwamnati, da dai sauran muhimman batutuwa.

Tsawon shekaru kafin 29 ga Mayu, 2023, Dauda Lawal ya kasance mai gidana – mutum ne da ya saba kiran kowane ma’aikacinsa ‘dan uwana.’ Babu wani mukami  a duniya da zai iya canja karamci da mutuntakar Dauda Lawal.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Duk da cewa ranar 2 ga watan Satumba ba ranar tattauna dimbin nasarorin da Gwamna Dauda Lawal ya samu ba ne a matsayin gwamnan Zamfara a cikin shekarar da ta gabata, domin an yi ta yada su a kafafen yada labarai.

Yau rana ce da ta ya fi dacewa a bayyana salon jagoranci da halayen Gwamna Lawal. Idan har kana da abubuwa da yawa da za ka bayyana, zai fi dacewa ka takaita, domin wasu bayanai na bukatar littafi ne (ina aiki a kan hakan. Littafi ne da zai wayar da kan mutane da dama).

Mai gidana Dauda Lawal mai saurare ne. Yana da salon da Shugaban Amurka na 30, Calbin Coolidge, yake cewa, ‘Duk nagartaccen mutum ya kasance mai saurare.’

Ga Margaret J. Wheatley, ta ce, saurare yana matsar da mu kusa da al’umma kuma yana taimaka mana mu zama cikakkun mutane, maau lafiya, kuma masu hankali. Rashin sauraro yana haifar da rarrabuwa, kuma rarrabuwa shi ne tushen duk wani wahala.

Mai gidana, Dauda Lawal, Allah Ya yi masa da kusan komai. Na sha ji yana fadin cewa da a ce an ba shi damar tsara rayuwarsa, ba zai iya tsara ta da dimbin ni’imomin da Allah Ya yi masa ba.

Mai gidana shi ne shahararre Dauda, wanda ya kasance abin yabo a gari. Sau da yawa mutane sukan yi hasashen da bai daidai ba wajen auna dukiyarsa, bk Naira kadai ba, har da dalar Amurka. Mai kamala da kyan hali, Dauda Lawal a kullum yana fitowa tamkar matashi mai shekaru arba’in da haihuwa saboda ya san saka sutura, hakkun!

Ba kamar sauran mutane masu irin mukamin sa ba, ya ba ya jijinda kai. Mai gida na, mai tawali’u ne, mai janyo mutane kusa da shi,  karbar al’umma. Yana karfafa ma’aikatansa sosai don su fadi ra’ayoyinsu. Yana shirya taruka na kai-tsaye tare da kananan jami’ai, masu tsaron kofa, direbobi, masu kula da tsirrai, da masu goge-goge don sauraron ra’ayoyinsu game da yanayin aiki da duk wata damuwa da suke da ita.

Kasancewar mai gidana Dauda Lawal mai sanin makamar aiki ne, ya san duk abin da ke gudanar a cikin gwamnatin sa. Kwamishinoni, masu ba da shawara, da sauran manyan jami’an tawagarsa suna taka tsantsan a cikin ayyukansu domin yana da masaniya a kan komai. Kofofinsa a bude suke, kuma ana iya samun wayarsa a koda yaushe (Ina tsammanin ma kusan kowa yana da lambar wayarsa). Gidan Dauda shi ne mafi saukin shiga idan aka kwatanta da gidajen wasu gwamnoni.

Dauda Lawal mai kyauta ne mai fara’a. Shi ya sa mutanen da suka fi shan wahala a gwamnatinsa su ne wadanda ke fama da matsalar ‘Sadistic Personality Disorder’ (kadan ne ma, idan akwai). Akwai mutaben da a kullum su na cikin fushi da bakin ciki saboda mai gidana Dauda Lawal, yana jin dadin bayarwa, taimako, da sanya murmushi a fuskokin al’umma. Wani abu mai dadi shi ne babu wanda zai iya tilasta masa ya yi abin da ba daidai ba (ma’ana, ba a masa abin da Bahaushe ke cewa ‘Ba a mugun sarki sai dai mugun bafade’). Babu! Kar ka yarda wani ya yi maka karya.

Idan kana son ka bata garrin ka a gaban Dauda Lawal, ka tunkare shi da tsegumi da ’yan kananan maganganu. Yana daraja ikhlasi kuma ba ya son fasikanci da rashi gaskiya. Yayan yawan cewa ba ya son aiki ‘kiya’. Kwararre ne wanda ke da kwarawa sosai a harkokin sa.

A duk lokacin da na shafe tare da shi, na san cewa mai gidana yana saurin fushi da mutanen da ba su da tsafta. Yana son tsafta sosai kuma yakan jaddada muhimmancin goge hakora da yin amfani da tuaren jiki na ‘deodorants’ da turaren kaya mai kamshi mai dadi ba mai hawa kai ba. Bai zai yiwu a kusanci shi da warin baki ko warin jiki ba; abu ne da zai masa dadi ba.

Yayin da ka ke cika shekaru 59 a daniya a yau, ina so ka sani cewa mutane da yawa su na sha’awar salon ka kuma suna girmama ka. Ka samu mutuntakar ka wajen ayyukan taimako a bangaren kamfanoni masu zaman kansu, kuma yanzu ka kafa tarihi a matsayinka na jagoran tawagar ceto Zamfara. Barka da Ranar Haihuwarka, Gamjin Zamfara!

Sulaiman Bala Idris shi ne Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DareDauda DareZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

Next Post

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

2 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

6 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

7 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

7 months ago
BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

7 months ago
Dauda
Ra'ayoyi

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

9 months ago
Next Post
Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.