• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Dimokradiyya Irin Ta Amurka’ Ta Bar Iraki Cikin Rugujewa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
‘Dimokradiyya Irin Ta Amurka’ Ta Bar Iraki Cikin Rugujewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 29 ga watan Agusta, wani mummunan rikici ya barke a Bagadaza, babban birnin kasar Iraki, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 30, tare da jikkata daruruwa. Hatta yankin “Green Zone” da sojojin Amurka ke ba da kariya, an kai musu hari da rokoki.

Jaridar New York Times ta ce, mai yiwuwa hakan na iya zama mafarin wani yanayi mafi hadari ga Iraki.

  • Gwamnatin Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan 10 Ga Manoma Domin Tabbatar Da Shuka Da Girbin Hatsi A Lokacin Kaka

Tun bayan zaben da aka yi bisa tsarin “dimokiradiyya irin ta Amurka” a Iraki a shekara ta 2005, ba a taba samun nasarar kafa gwamnati ba.

Amurka

Bayan kusan shekaru 20 da fara aiwatar da abin da aka kira “Gyare-gyaren demokradiyya”, matakin ya lalata Iraki kwarai da gaske.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A fagen siyasa, Amurka ta shigar da tsarin siyasar dimokuradiyya na yammacin duniya zuwa cikin Iraki, wanda a zahiri ya haifar da rarrabuwar kawuna a fannin siyasar kasar, kuma da wuya bangarorin siyasa daban-daban su cimma nasarar sulhu.

Ta fuskar tattalin arziki, yake-yake da tashe-tashen hankula sun haifar da asarar da ba za a iya misaltawa ba ga tattalin arzikin Iraki.

Alkaluman sun nuna cewa, a shekarar 1990, GDP na kowane mutum a Iraki ya kai dala 10,356, amma ya zuwa shekarar 2020, adadin ya yi kasa zuwa dala 4,157 kacal.

A fannin tsaro, saboda rudanin siyasar da aka samu a cikin gidan a Iraki, ta’addanci ya bazu cikin sauri, kuma al’ummar kasar sun sake zama wadanda abin ya shafa kai tsaye.

Ahmed al-Sharifi, kwararre kan al’amuran da suka shafi dabarun Iraki ya yi nuni da cewa, manufar mamayar da Amurka ta yi a Iraki, ba wai don a taimaka wa Irakin wajen tabbatar da dimokuradiyya kamar yadda ta fada ba ne, sai dai don karfafa ikon Amurka a yankin gabas ta tsakiya.

A cikin shekaru 20 da suka gabata, mutane kusan miliyan daya a Gabas ta Tsakiya, sun fada karkashin rugujewar gidaje irin na “dimokradiyyar Amurka”.

Dole ne kasashen duniya su yi la’akari da laifukan da Amurka ta aikata a Gabas ta Tsakiya, tare da neman adalci ga wadanda suka yi hasara sakamakon hakan. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Da Ya Kashe Iyayensa Da Tabarya A Jigawa

Next Post

Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai – Dakta Yakubu

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

10 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

11 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

13 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

16 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

17 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

18 hours ago
Next Post
Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai – Dakta Yakubu

Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai - Dakta Yakubu

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.