ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Dimokradiyya Irin Ta Amurka’ Ta Bar Iraki Cikin Rugujewa

by CMG Hausa
4 years ago
Amurka

A ranar 29 ga watan Agusta, wani mummunan rikici ya barke a Bagadaza, babban birnin kasar Iraki, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 30, tare da jikkata daruruwa. Hatta yankin “Green Zone” da sojojin Amurka ke ba da kariya, an kai musu hari da rokoki.

Jaridar New York Times ta ce, mai yiwuwa hakan na iya zama mafarin wani yanayi mafi hadari ga Iraki.

  • Gwamnatin Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan 10 Ga Manoma Domin Tabbatar Da Shuka Da Girbin Hatsi A Lokacin Kaka

Tun bayan zaben da aka yi bisa tsarin “dimokiradiyya irin ta Amurka” a Iraki a shekara ta 2005, ba a taba samun nasarar kafa gwamnati ba.

ADVERTISEMENT

Amurka

Bayan kusan shekaru 20 da fara aiwatar da abin da aka kira “Gyare-gyaren demokradiyya”, matakin ya lalata Iraki kwarai da gaske.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

A fagen siyasa, Amurka ta shigar da tsarin siyasar dimokuradiyya na yammacin duniya zuwa cikin Iraki, wanda a zahiri ya haifar da rarrabuwar kawuna a fannin siyasar kasar, kuma da wuya bangarorin siyasa daban-daban su cimma nasarar sulhu.

Ta fuskar tattalin arziki, yake-yake da tashe-tashen hankula sun haifar da asarar da ba za a iya misaltawa ba ga tattalin arzikin Iraki.

Alkaluman sun nuna cewa, a shekarar 1990, GDP na kowane mutum a Iraki ya kai dala 10,356, amma ya zuwa shekarar 2020, adadin ya yi kasa zuwa dala 4,157 kacal.

A fannin tsaro, saboda rudanin siyasar da aka samu a cikin gidan a Iraki, ta’addanci ya bazu cikin sauri, kuma al’ummar kasar sun sake zama wadanda abin ya shafa kai tsaye.

Ahmed al-Sharifi, kwararre kan al’amuran da suka shafi dabarun Iraki ya yi nuni da cewa, manufar mamayar da Amurka ta yi a Iraki, ba wai don a taimaka wa Irakin wajen tabbatar da dimokuradiyya kamar yadda ta fada ba ne, sai dai don karfafa ikon Amurka a yankin gabas ta tsakiya.

A cikin shekaru 20 da suka gabata, mutane kusan miliyan daya a Gabas ta Tsakiya, sun fada karkashin rugujewar gidaje irin na “dimokradiyyar Amurka”.

Dole ne kasashen duniya su yi la’akari da laifukan da Amurka ta aikata a Gabas ta Tsakiya, tare da neman adalci ga wadanda suka yi hasara sakamakon hakan. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya
Daga Birnin Sin

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Next Post
Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai – Dakta Yakubu

Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai - Dakta Yakubu

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.