• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diphtheria: Gwamnatin Kano Ta Yi Gargadi Kan Hada Taruka

by Sadiq
2 years ago
Diphtheria

Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf ya yi kira ga jama’a da su guji zuwa taruka da ba dole ba domin kare kansu da sauran jama’a daga kamuwa da cutar diphtheria.

Dakta Labaran ya yi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Laraba.

  • Shirin Tsige Fubara: Gwamnonin PDP Za Su Gana Da Wike A Abuja
  • Hatsarin Kwale-Kwale: Har Yanzu Ana Neman Mutane Sama Da 70 A Taraba – NEMA

A cewarsa, ya zama wajibi wajen wayar da kan jama’a kan wajibcin daukar matakan kariya da nufin dakile yaduwar cutar diphtheria a jihar Kano.

Kwamishinan ya ce cutar diphtheria cuta ce da ke yaduwa ta iska, don haka duk mutumin da ake zargin ya kamu da cutar ko kuma yake dauke da alamun cutar da su ziyarci likita don duba su.

Ya jaddada cewa a guji cudanya ta hanyar musabaha ko atishawa da mutane masu dauke da alamun cutar, inda ya bayyana cewa wadannan su ne manyan hanyoyin yada cutar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

Dakta Labaran ya ba da shawarar cewa idan yaro ne ya kamu da cutar, kada iyaye su bari ya je makaranta su gaggauta kai shi asibiti don yi masa gwaje-gwaje da duba lafiyarsa.

Kwamishinan ya gargadi mutane da su daina hada taruka marasa amfani musamman ganin yadda lokacin sanyi ke karatowa, lamarin da ka iya ta’azzara cutar diphtheria.

Ya kara da cewa idan taro ya zama wajibi, to ya kamata a yi a waje mai ishasshiyar iska.

Dokta Labaran ya bayyana cewa, babbar hanyar kariya daga cutar diphtheria ita ce allurar rigakafi, ya kuma yi kira ga iyaye da su tabbatar da an yi wa ‘ya’yansu masu shekaru hudu zuwa 14 rigakafin sau uku a jere, domin kare su daga kamuwa daga cutar.

Har wa yau ya bayyana cewa idan yaro ya kamu da cutar amai da gudawa, dole ne a yi wa dukkan ‘yan uwansa allurar rigakafi don kare shi daga diphtheria da kuma wasu cututtuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
Labarai

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Next Post
Suswam

Kotun Daukaka Kara Ta Tsige Suswam Daga Kujerar Sanata 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.