• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

by Rabilu Sanusi Bena, Sulaiman and Rabilu Sani Bena
3 months ago
Siyasa

Sabon shugaban riko na kungiyar masu shirya fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN), Alhaji Shehu Hassan Kano ya bayyana cewa; yanzu lokaci ne da ya kamata masana’antar Kannywood ta hada kai da ‘yan siyasa, musamman wadanda ke rike da mulki; domin sama wa masana’antar ci gaba mai dorewa, a wata hira da ya yi da FIM, Shehu Hassan, wanda shi ne ya maye gurbin tsohon shugaban kungiyar, Malam Mai Kudi (Cashman), wanda ya rasu a kwanakin baya ya bayyana cewa; kowa da kowa nasu ne a MOPPAN.

“Ba jam’iyya za mu shiga ba, ba kuma wani bangare na siyasa za mu yi ba, ita masana’antar Kannywood, akwai ‘yan siyasa, kuma ba jam’iyya daya suke yi ba, za ka ga wasu suna wannan jam’iyar; yayin da wasu kuma za su zabi wata jam’iyyar daban, don haka, mu a tsarinmu na MOPPAN, kowa namu ne, dan masana’antarmu ne, duk wanda ya ga akwai wani abu da za a yi harkar fim ta ci gaba, ya kawo mana shi, mu nan a kungiyance za mu shige gaba wajen ganin wannan abu ya tabbata”, in ji Hassan Kano.

  • Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Har ila yau, ya ci gaba da bayyana cewa; don haka, mu ba wani bangare guda daya za mu bi mu rike ba, domin kuwa yin hakan; akwai hadari, so muke in dai dan fim ne, duk wata tafiya da yake yi ta siyasa; ya zamana ya amfana da tafiyar, ita ma masana’antar ta amfana, ko da kuwa ba jam’iyyarsa ba ce take mulki, za mu hadu ne a matsayin ‘yan fim mu amfana da junanmu a wajen tafiyar siyasa.

Wannnan na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara kada gangar siyasa a Nijeriya, kwanaki dai an hangi wasu jarumai a masana’antar Kannywood, sun kai ziyara har gida ga tsohon mataimakin shugaban kasa, kuma tsohon dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyar PDP, a babban zaben da ya gabata, Alhaji Atiku Abubakar (Wazirin Adamawa).

Hakan yasa wasu ke ganin hakan bai dace ba, ganin cewa; Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta bugi kirjin yi wa masana’antar Kannywood gata, ta hanyar bai wa wasu daga cikin jaruman masana’antar Kannywood manya-manyan mukamai a gwamnati, ciki har da Babban Manajin Darakta na Hukumar Fina-finai ta Nijeriya (NFC).

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Koma dai mene ne, Shehu Hassan Kano ya ce; ba za su takurawa kowa a cikin ‘yan kungiyar ta MOPPAN, wajen yin ra’ayin siyasar da suka ga dama ba, sai dai, ya ce duk wanda zai yi siyasa ya fara dubawa idan akwai mafita, sai ya shiga idan kuma babu sai ya hakura ya canza wata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna
Labarai

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.