• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ran 22 ga wata, gwamnatin Japan ta sanar da cewa, za ta zubar da ruwan dagwalon nukiliyar da take ajiye da shi cikin teku, tun daga gobe Alhamis 24 ga wata. Ta yi biris da rashin jin dadin da jama’ar duniya ke nunawa kan hakan, inda ta sanya jama’ar duniya tunkarar asarar da matakin nata zai haifar.

Jami’ar Tsinghua ta kasar Sin ta yi hasashen cewa, bisa gwajin da ta yi, idan wannan ruwa ya shiga teku, zai isa gabar tekun kasar Sin bayan kwanaki 240, yayin da zai isa gabar tekun arewacin nahiyar Amurka cikin kwanaki 1200. Bayan shekaru 10 kuma, zai shafi dukkanin fadin teku a duniya. Matakin da Japan ke dauka, ba zai nisanta ita kanta da bala’in ba.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

A hakika dai, shirin zai kawowa sha’anin kamun kifi a kasar Japan kalubaloli da dama. Hukuma mai kula da kayayyakin gona, da gandun daji, da teku, ta ba da kididdiga ta shekarar 2022, cewa yawan albarkatun teku da ake samu sun yi kasa tun daga shekarar 1956.

Ban da wannan kuma, kasashe ko yankuna 12, sun yanke shawarar hana shigar da kayayyakin teku daga Fukushima na Japan. Idan gwamnatin Japan ta aikata wannan shiri, to ba shakka kasashen duniya za su kara kayyade shigar da albarkatun teku, da abincin dake da nasaba da hakan daga kasar Japan, lamarin da zai kawo illar ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar.

Al’ummomin kasar Japan, kungiyoyin kasashen duniya, da kasashen dake kewayen tekun Pacific sun yi Allah wadai da batun da kakkausar harshe, inda suka bukaci gwamnatin kasar Japan da ta soke wannan kuduri. Gamayyar kasa da kasa na ganin cewa, batun zubar da ruwan dagwalon nukuliya cikin teku ya saba wa dokar kasa da kasa, kuma zai haddasa matsalolin da ba za a iya warware su ba.

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Tun lokacin da kasar Japan ta gabatar da wannan shiri yau shekaru 2 da suka gabata, mutanen kasa da kasa suka nuna shakku da damuwa matuka kan ko shirin ya dace da doka ko a’a, ko kuma yana da tsaro ko a’a. Domin sassauta damuwar jama’a, gwamnatin kasar Japan da kamfanin wutar lantarki na Tokyo sun yi alkawari cewa, ba za su zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku ba, in babu amincewar bangarorin da abin ya shafa kan wannan batu. Amma, mutuncin gwamnatin kasar Japan ya zube sabo da ba ta cika alkawarinta ba.

Ba kawai gwamnatin kasar Japan ta yi karya ga al’ummunta ba, har ma ta yi karya ga gamayyar kasa da kasa cewar, wai shirin zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku ba zai haifar da matsala ba. A dayan bangare, kasar Japan ta canja ma’anar ruwan dagwalon nukiliya zuwa ruwan tsabtacen nukiliya, domin boye illar da ruwan zai haifar wa al’ummun duk duniya. haka kuma, kasar Japan ta kashe kudade da yawa domin sayan “iznin amincewa” kan shirinta.

Kana, bisa dokar teku ta MDD, kasashen duniya suna da hakkin kiyaye muhallin teku, a matsayin daya daga kasashen da suka sa hannu kan dokar, ya kamata kasar Japan ta dauki alhakinta yadda ya kamata. Kuma, gamayyar kasa da kasa suna da ikon kare kansu bisa doka, da kuma neman diyya daga kasar Japan.

Duniya gidan daukacin bil Adama ne, kuma tsaron teku, da nagartattun muhallinsa, na amfanar jama’a matuka. Shirin da Japan take bi, zai sanya dukkanin fadin duniya yin asara. Ana fatan gwamnatin Japan za ta dakatar da wannan shiri, wanda ba wanda zai ci gajiyarsa, ta kuma nemi wata hanya da ta dace, kada ’yan siyasar kasar sun kare moriyar kansu ta bangarensu kadai, ta sanya duniya cikin mawuyacin hali. (Mai zana MINA Masu Fassara: MINA, Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Da Hanzarta Fadada BRICS Da Kuma Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Daukacin Bil Adama A Zahiri

Next Post

Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Related

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

46 minutes ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

18 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

21 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

22 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Next Post
Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.