• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

byCMG Hausa
2 years ago
Japan

Ran 22 ga wata, gwamnatin Japan ta sanar da cewa, za ta zubar da ruwan dagwalon nukiliyar da take ajiye da shi cikin teku, tun daga gobe Alhamis 24 ga wata. Ta yi biris da rashin jin dadin da jama’ar duniya ke nunawa kan hakan, inda ta sanya jama’ar duniya tunkarar asarar da matakin nata zai haifar.

Jami’ar Tsinghua ta kasar Sin ta yi hasashen cewa, bisa gwajin da ta yi, idan wannan ruwa ya shiga teku, zai isa gabar tekun kasar Sin bayan kwanaki 240, yayin da zai isa gabar tekun arewacin nahiyar Amurka cikin kwanaki 1200. Bayan shekaru 10 kuma, zai shafi dukkanin fadin teku a duniya. Matakin da Japan ke dauka, ba zai nisanta ita kanta da bala’in ba.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

A hakika dai, shirin zai kawowa sha’anin kamun kifi a kasar Japan kalubaloli da dama. Hukuma mai kula da kayayyakin gona, da gandun daji, da teku, ta ba da kididdiga ta shekarar 2022, cewa yawan albarkatun teku da ake samu sun yi kasa tun daga shekarar 1956.

Ban da wannan kuma, kasashe ko yankuna 12, sun yanke shawarar hana shigar da kayayyakin teku daga Fukushima na Japan. Idan gwamnatin Japan ta aikata wannan shiri, to ba shakka kasashen duniya za su kara kayyade shigar da albarkatun teku, da abincin dake da nasaba da hakan daga kasar Japan, lamarin da zai kawo illar ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar.

Al’ummomin kasar Japan, kungiyoyin kasashen duniya, da kasashen dake kewayen tekun Pacific sun yi Allah wadai da batun da kakkausar harshe, inda suka bukaci gwamnatin kasar Japan da ta soke wannan kuduri. Gamayyar kasa da kasa na ganin cewa, batun zubar da ruwan dagwalon nukuliya cikin teku ya saba wa dokar kasa da kasa, kuma zai haddasa matsalolin da ba za a iya warware su ba.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Tun lokacin da kasar Japan ta gabatar da wannan shiri yau shekaru 2 da suka gabata, mutanen kasa da kasa suka nuna shakku da damuwa matuka kan ko shirin ya dace da doka ko a’a, ko kuma yana da tsaro ko a’a. Domin sassauta damuwar jama’a, gwamnatin kasar Japan da kamfanin wutar lantarki na Tokyo sun yi alkawari cewa, ba za su zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku ba, in babu amincewar bangarorin da abin ya shafa kan wannan batu. Amma, mutuncin gwamnatin kasar Japan ya zube sabo da ba ta cika alkawarinta ba.

Ba kawai gwamnatin kasar Japan ta yi karya ga al’ummunta ba, har ma ta yi karya ga gamayyar kasa da kasa cewar, wai shirin zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku ba zai haifar da matsala ba. A dayan bangare, kasar Japan ta canja ma’anar ruwan dagwalon nukiliya zuwa ruwan tsabtacen nukiliya, domin boye illar da ruwan zai haifar wa al’ummun duk duniya. haka kuma, kasar Japan ta kashe kudade da yawa domin sayan “iznin amincewa” kan shirinta.

Kana, bisa dokar teku ta MDD, kasashen duniya suna da hakkin kiyaye muhallin teku, a matsayin daya daga kasashen da suka sa hannu kan dokar, ya kamata kasar Japan ta dauki alhakinta yadda ya kamata. Kuma, gamayyar kasa da kasa suna da ikon kare kansu bisa doka, da kuma neman diyya daga kasar Japan.

Duniya gidan daukacin bil Adama ne, kuma tsaron teku, da nagartattun muhallinsa, na amfanar jama’a matuka. Shirin da Japan take bi, zai sanya dukkanin fadin duniya yin asara. Ana fatan gwamnatin Japan za ta dakatar da wannan shiri, wanda ba wanda zai ci gajiyarsa, ta kuma nemi wata hanya da ta dace, kada ’yan siyasar kasar sun kare moriyar kansu ta bangarensu kadai, ta sanya duniya cikin mawuyacin hali. (Mai zana MINA Masu Fassara: MINA, Maryam Yang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version