• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ran 22 ga wata, gwamnatin Japan ta sanar da cewa, za ta zubar da ruwan dagwalon nukiliyar da take ajiye da shi cikin teku, tun daga gobe Alhamis 24 ga wata. Ta yi biris da rashin jin dadin da jama’ar duniya ke nunawa kan hakan, inda ta sanya jama’ar duniya tunkarar asarar da matakin nata zai haifar.

Jami’ar Tsinghua ta kasar Sin ta yi hasashen cewa, bisa gwajin da ta yi, idan wannan ruwa ya shiga teku, zai isa gabar tekun kasar Sin bayan kwanaki 240, yayin da zai isa gabar tekun arewacin nahiyar Amurka cikin kwanaki 1200. Bayan shekaru 10 kuma, zai shafi dukkanin fadin teku a duniya. Matakin da Japan ke dauka, ba zai nisanta ita kanta da bala’in ba.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

A hakika dai, shirin zai kawowa sha’anin kamun kifi a kasar Japan kalubaloli da dama. Hukuma mai kula da kayayyakin gona, da gandun daji, da teku, ta ba da kididdiga ta shekarar 2022, cewa yawan albarkatun teku da ake samu sun yi kasa tun daga shekarar 1956.

Ban da wannan kuma, kasashe ko yankuna 12, sun yanke shawarar hana shigar da kayayyakin teku daga Fukushima na Japan. Idan gwamnatin Japan ta aikata wannan shiri, to ba shakka kasashen duniya za su kara kayyade shigar da albarkatun teku, da abincin dake da nasaba da hakan daga kasar Japan, lamarin da zai kawo illar ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar.

Al’ummomin kasar Japan, kungiyoyin kasashen duniya, da kasashen dake kewayen tekun Pacific sun yi Allah wadai da batun da kakkausar harshe, inda suka bukaci gwamnatin kasar Japan da ta soke wannan kuduri. Gamayyar kasa da kasa na ganin cewa, batun zubar da ruwan dagwalon nukuliya cikin teku ya saba wa dokar kasa da kasa, kuma zai haddasa matsalolin da ba za a iya warware su ba.

Labarai Masu Nasaba

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Tun lokacin da kasar Japan ta gabatar da wannan shiri yau shekaru 2 da suka gabata, mutanen kasa da kasa suka nuna shakku da damuwa matuka kan ko shirin ya dace da doka ko a’a, ko kuma yana da tsaro ko a’a. Domin sassauta damuwar jama’a, gwamnatin kasar Japan da kamfanin wutar lantarki na Tokyo sun yi alkawari cewa, ba za su zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku ba, in babu amincewar bangarorin da abin ya shafa kan wannan batu. Amma, mutuncin gwamnatin kasar Japan ya zube sabo da ba ta cika alkawarinta ba.

Ba kawai gwamnatin kasar Japan ta yi karya ga al’ummunta ba, har ma ta yi karya ga gamayyar kasa da kasa cewar, wai shirin zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku ba zai haifar da matsala ba. A dayan bangare, kasar Japan ta canja ma’anar ruwan dagwalon nukiliya zuwa ruwan tsabtacen nukiliya, domin boye illar da ruwan zai haifar wa al’ummun duk duniya. haka kuma, kasar Japan ta kashe kudade da yawa domin sayan “iznin amincewa” kan shirinta.

Kana, bisa dokar teku ta MDD, kasashen duniya suna da hakkin kiyaye muhallin teku, a matsayin daya daga kasashen da suka sa hannu kan dokar, ya kamata kasar Japan ta dauki alhakinta yadda ya kamata. Kuma, gamayyar kasa da kasa suna da ikon kare kansu bisa doka, da kuma neman diyya daga kasar Japan.

Duniya gidan daukacin bil Adama ne, kuma tsaron teku, da nagartattun muhallinsa, na amfanar jama’a matuka. Shirin da Japan take bi, zai sanya dukkanin fadin duniya yin asara. Ana fatan gwamnatin Japan za ta dakatar da wannan shiri, wanda ba wanda zai ci gajiyarsa, ta kuma nemi wata hanya da ta dace, kada ’yan siyasar kasar sun kare moriyar kansu ta bangarensu kadai, ta sanya duniya cikin mawuyacin hali. (Mai zana MINA Masu Fassara: MINA, Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Kira Da Hanzarta Fadada BRICS Da Kuma Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Daukacin Bil Adama A Zahiri

Next Post

Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Related

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

1 hour ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

1 hour ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

5 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

7 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

7 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

24 hours ago
Next Post
Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

Wagner Yevgeny Prigozhin Ya Mutu A Hatsarin Jirgin Saman Rasha

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.