• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Hana Zanga-Zanga, Shugaba Tinubu Ya Amince Da Kafa Ofishin Matasa A Abuja

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Zanga-Zanga

Shugaba Bola Tinubu ya amince da kafa ma’aikatar harkokin Matasa a Abuja (FCT), a cewar Ministan babban birnin tarayya Nyesom Wike. An bayyana hakan ne yayin wata ganawa da mazauna ƙaramar hukumar Bwari, a wani yunkuri na Minista Wike na ci gaba da samar da zaman lafiya a yayin da ake shirin gudanar da zanga-zangar ƙasa baki ɗaya daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta.

Wannan ganawar ta biyo bayan wasu tattaunawar a baya da aka yi a Gwagwalada, da Kuje, da Kwali, da ƙaramar hukumar birnin Abuja (AMAC), da Abaji don hana matasa shiga zanga-zangar.

  • Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja
  • An Tona Asirin Masu Yi Wa Matatar Dangote Zangon Ƙasa

Wike ya amince da wannan buƙata ne a lokacin da matasan AMAC suka gabatar masa da ita, wanda ya yi alƙawarin tattaunawa da Shugaba Tinubu. Ministan ya tabbatar da amincewar a lokacin ganawar a Bwari, yana mai jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da haɗin kan matasa da bunƙasa su. Ya yaba wa matasan bisa kin shiga zanga-zangar da ake shirin yi, yana ganin wannan mataki na nuna hazaƙa da goyon bayan gwamnati ne. Wike ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa za a ci gaba da inganta ababen more rayuwa, tare da kammala ayyukan hanyoyi a garuruwan wajen FCT nan da Disamba 2024.

A nasa jawabin, Mista Ezekiel Dalhatu, wanda ya wakilci ƙungiyar masu ruwa da tsaki ta Matasa da haɗin gwuiwar dukkan ƙungiyoyin matasa a FCT, ya tabbatar da cewa matasa sun yanke shawarar shiga tattaunawa maimakon zanga-zanga.

Ya jaddada muhimmancin tattaunawa mai ma’ana da gwamnati don magance matsalolinsu. Shugaban ƙaramar hukumar Bwari, Mista John Gabaya, ya yi kira ga matasa da su rungumi tattaunawa, yana mai tabbatar wa Wike da goyon bayan mazauna FCT.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

An kammala zaman ne da gabatar da hoton girmamawa na Wike daga matasa da sauran masu ruwa da tsaki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba
Labarai

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Next Post
Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.