• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Hana Zanga-Zanga, Shugaba Tinubu Ya Amince Da Kafa Ofishin Matasa A Abuja

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Don Hana Zanga-Zanga, Shugaba Tinubu Ya Amince Da Kafa Ofishin Matasa A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Tinubu ya amince da kafa ma’aikatar harkokin Matasa a Abuja (FCT), a cewar Ministan babban birnin tarayya Nyesom Wike. An bayyana hakan ne yayin wata ganawa da mazauna ƙaramar hukumar Bwari, a wani yunkuri na Minista Wike na ci gaba da samar da zaman lafiya a yayin da ake shirin gudanar da zanga-zangar ƙasa baki ɗaya daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta.

Wannan ganawar ta biyo bayan wasu tattaunawar a baya da aka yi a Gwagwalada, da Kuje, da Kwali, da ƙaramar hukumar birnin Abuja (AMAC), da Abaji don hana matasa shiga zanga-zangar.

  • Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja
  • An Tona Asirin Masu Yi Wa Matatar Dangote Zangon Ƙasa

Wike ya amince da wannan buƙata ne a lokacin da matasan AMAC suka gabatar masa da ita, wanda ya yi alƙawarin tattaunawa da Shugaba Tinubu. Ministan ya tabbatar da amincewar a lokacin ganawar a Bwari, yana mai jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da haɗin kan matasa da bunƙasa su. Ya yaba wa matasan bisa kin shiga zanga-zangar da ake shirin yi, yana ganin wannan mataki na nuna hazaƙa da goyon bayan gwamnati ne. Wike ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa za a ci gaba da inganta ababen more rayuwa, tare da kammala ayyukan hanyoyi a garuruwan wajen FCT nan da Disamba 2024.

A nasa jawabin, Mista Ezekiel Dalhatu, wanda ya wakilci ƙungiyar masu ruwa da tsaki ta Matasa da haɗin gwuiwar dukkan ƙungiyoyin matasa a FCT, ya tabbatar da cewa matasa sun yanke shawarar shiga tattaunawa maimakon zanga-zanga.

Ya jaddada muhimmancin tattaunawa mai ma’ana da gwamnati don magance matsalolinsu. Shugaban ƙaramar hukumar Bwari, Mista John Gabaya, ya yi kira ga matasa da su rungumi tattaunawa, yana mai tabbatar wa Wike da goyon bayan mazauna FCT.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

An kammala zaman ne da gabatar da hoton girmamawa na Wike daga matasa da sauran masu ruwa da tsaki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaNyesom Wike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sakamakon Zanga-Zanga MTN Ta Rufe Ofisoshinta Na Kasar Gaba Ɗaya 

Next Post

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

Related

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

49 minutes ago
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
Labarai

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

2 hours ago
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 
Labarai

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

2 hours ago
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

4 hours ago
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

5 hours ago
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Labarai

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

6 hours ago
Next Post
Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.