• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Abinda Na Yi A Rayuwata Bazata Ne – Obasanjo

by Sadiq
3 years ago
Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, a jiya ya bayyana cewa komai na rayuwarsa ya faru ne ta hanyar bazata wanda ya hada da zamansa a matsayin shugaban kasa a lokacin mulkin soja da kuma shugaban kasar Nijeriya a lokacin dimokuradiyya.

Tsohon shugaban kasar wanda ya zama bako na musamman a wani shiri na gidan rediyo mai zaman kansa a Abeokuta, ya ce in ban da noma da aka haife shi a ciki, wasu sun faru ne ta hanyar bazata, inda ya kara da cewa yana alfahari kasancewarsa manomi.

  • Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Sun Roki Manyan Kasashen Duniya Su Kawo Musu Dauki 
  • ‘Yan Sandan Birnin Milan Sun Ba Wa Dan Wasa Bukayoko Hakuri

Da yake amsa tambayoyi daga tsohon kyaftin din Super Eagles, Segun Odegbami, wanda ke jagorantar shirin Obasanjo ya jaddada cewa ba daidai ba ne kowa ya kira kansa manomi.

Ya ce, “Ba na so kalmar da kuka yi amfani da ita, ‘ soyayya da noma’, ni manomi ne. Me kuke nufi da soyayya? Duk abin da na yi a rayuwata ta hanyar bazata ne. Abin da ba bazata bane, shi ne noma. Duk sauran abubuwan da na kasance cikin bazata ne.

“Ka san yadda na fara. An haife ni a kauye. Na je makaranta ne bisa bazata. Mahaifina ya ce, ‘ba za ku samar da komai na daban ba? Shi yasa na shiga harkar noma.

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

“Idan aka duba kasashen da suka ci gaba, sun ci gaba ne a fannin noma. Na farko, don samar da abinci, na biyu don sarrafa abin da suke samu daga gonakinsu. Na uku, a ba da shi a matsayin fitar da shi zuwa kasashen waje, wanda shi ne manufar samun kudin waje.

“Kuma hanyar samar da ayyukan yi ne ga matasa”.

Obasanjo wanda ya shawarci matasan Nineriya da su karbi mukaman shugabanci a yanzu, ya bukace su da kada su bari wani ya yaudare su da sunan su manyan gobe ne.

Ya ce wasu gurbatattun shugabanni za su ruguza abin da ake kira gobe idan matasa suka kasa tashi tsaye su dauki makomarsu a hannunsu.

“Shawarata ga matasan Nijeriya ita ce, kada ku bari wani ya ce muku ku ne shugabannin gobe. Za ku jira goben kafin ku karbi ragamar shugabancin, to gobe ba za ta zo ba. Wannan lokaci ne da ya kamata matasa su tashi su tabbatar da hakan,” inji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Next Post
De Ligt Ya Koma Bayern Munchen Daga Juventus

De Ligt Ya Koma Bayern Munchen Daga Juventus

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.