• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Éric Sékou Chelle: Sabon Kociyan Super Eagles

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
Chelle

A satin da ya gabata ne hukumar kwallon kafar Nijeriya, NFF ta tabbatar da daukar Éric Sékou Chelle a matsayin sabon kocin kungiyar kwallan kafa ta Super Eagles kuma kamar yadda sanarwar ta tabbatar nadin Chelle ya fara aiki ne nan take inda a cewar hukumar NFF ta yanke shawarar daukar sabon kocin ne daga ketare a zaman da ta yi ranar 2 ga watan Janairun wannan shekarar ta 2025.

NFF ta ce babban aikin da ta dora wa tsohon kocin dan asalin kasar Mali shi ne: kai Nijeriya Gasar Kofin Duniya ta 2026, abin da masana kwallon kafa a nahiyar Afirka da ma Nigeriya suke ganin da kamar wuya ganin yadda rukunin da Nigeriya take ciki yake da kuma kalubalen da ke gaban samun tikitin zuwa gasar ta cin kofin duniya da zai fara jagorantar Nigeriya a cikin wannan shekarar.

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Waye Éric Sékou Chelle

Ba kamar sauran fitattu a harkar kwallon kafar Afirka, irin su George Weah da Abedi Pele da Samuel Eto’o da Rashidi Yekini da sauransu ba, Eric Chelle ba fitacce ba ne a kwallon kafar Afirka, dalili kuwa shi ne a lokacin da yake dan wasa bai wani shahara sosai ba saboda a lokacin da yake buga wasa, sau biyar kawai ya buga wa babbar tagawar kwallon kwallon kafar kasarsa, Mali wasa. Dangane da matakin kungiyoyi kuwa, ya buga wasa ne yawanci a kananan kungiyoyin Faransa, irin su Martigues da Balenciennes da Lens da Istres da kuma Chamois Niortais. To sai dai Chelle ya bai wa mutane da dama mamaki a matakin koci saboda irin kokarin da ake ganin ya yi domin kafin ya zama kocin babbar tawagar Mali, ya rike wasu kungiyoyin Faransa da ke buga karamar gasar kasar.

Chelle, mai shekara 47 ya samu kwarewa a aikin horarwa ne a kungiyoyin GS Consolat, FC Martigues, MC Oran and Boulogne kuma a shekarar 2022 ce Mali ta nada shi a matsayin wanda zai jagoranci babbar tawagar kasar, kuma ya bayar da mamaki bayan ya kai kasar gasar cin Kofin Afirka ta 2023 da aka gudanar a Ibory Coast inda a gasar ce, Mali ta samu nasarar kai wa matakin kwata-fainal, kafin mai masaukin baki ta fitar da ita a karin lokaci, sai dai bayan gasar ne kasar ta kore shi a watan Yunin 2024.

LABARAI MASU NASABA

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

‘Rike Super Eagle ba karamin aiki ba ne’

Amma kuma aikin horar da Nijeriya babban aiki ne da ke bukatar kwarewa da jajircewar koci, la’akari da yadda kasar nan ke da fitattun ‘yan wasa da ke buga wasa a wasu manyan kungiyoyin Turai wanda hakan yake nufin ko a wajen gayyatar ‘yan wasa akwai babban aiki a wajen mai koyar da tawagar Nigeriya saboda akwai ‘yan wasa da yawa kuma suna kokarin da ya kamata a gayyace su.

To amma duk da kwararrun ‘yan wasa da kasar nan ke da su, tana fama da matsalar samun nasarorin da ake bukata a wasanninta, musamman a Afirka kuma mutane da alama na alakanta rashin katabus da Super Eagle ke yi da rashin kwararren koci, wanda zai iya hada fitattun ‘yanwasan da kasar ke da su domin hada tawaga mai karfin da za ta lashe babbar gasa.

Masu koyarwa da dama – na ciki da wajen kasar nan sun zo, sun kuma tafi, amma babbar tambayar da ke yawo a bakunan ‘yan Nigeriya, shi ne shin

Eric Chelle zai iya fitar wa Super Eagles kitse daga wuta?

Cikin sanarwar nadin nasa, NFF ta dora masa alhakin kai Nijeriya gasar Kofin Duniya domin a yanzu haka kasar nan na matsayi na biyar a kan teburin neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026 da maki uku, bayan da ta ji jiki a hannun Benin da Lesotho sannan wasannin farko da Chelle zai fuskanta a neman gurbin Gasar Kofin Duniya ta 2026 su ne a watan Maris inda zai buga wasanni biyu. Amma kuma a yanzu hankula sun koma kan sabon kocin domin ganin irin rawar da zai taka wajen farfado da Super Eagles.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara
Wasanni

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu
Wasanni

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Next Post
Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.