• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Éric Sékou Chelle: Sabon Kociyan Super Eagles

by Abba Ibrahim Wada
5 months ago
in Wasanni
0
Éric Sékou Chelle: Sabon Kociyan Super Eagles
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A satin da ya gabata ne hukumar kwallon kafar Nijeriya, NFF ta tabbatar da daukar Éric Sékou Chelle a matsayin sabon kocin kungiyar kwallan kafa ta Super Eagles kuma kamar yadda sanarwar ta tabbatar nadin Chelle ya fara aiki ne nan take inda a cewar hukumar NFF ta yanke shawarar daukar sabon kocin ne daga ketare a zaman da ta yi ranar 2 ga watan Janairun wannan shekarar ta 2025.

NFF ta ce babban aikin da ta dora wa tsohon kocin dan asalin kasar Mali shi ne: kai Nijeriya Gasar Kofin Duniya ta 2026, abin da masana kwallon kafa a nahiyar Afirka da ma Nigeriya suke ganin da kamar wuya ganin yadda rukunin da Nigeriya take ciki yake da kuma kalubalen da ke gaban samun tikitin zuwa gasar ta cin kofin duniya da zai fara jagorantar Nigeriya a cikin wannan shekarar.

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Waye Éric Sékou Chelle

Ba kamar sauran fitattu a harkar kwallon kafar Afirka, irin su George Weah da Abedi Pele da Samuel Eto’o da Rashidi Yekini da sauransu ba, Eric Chelle ba fitacce ba ne a kwallon kafar Afirka, dalili kuwa shi ne a lokacin da yake dan wasa bai wani shahara sosai ba saboda a lokacin da yake buga wasa, sau biyar kawai ya buga wa babbar tagawar kwallon kwallon kafar kasarsa, Mali wasa. Dangane da matakin kungiyoyi kuwa, ya buga wasa ne yawanci a kananan kungiyoyin Faransa, irin su Martigues da Balenciennes da Lens da Istres da kuma Chamois Niortais. To sai dai Chelle ya bai wa mutane da dama mamaki a matakin koci saboda irin kokarin da ake ganin ya yi domin kafin ya zama kocin babbar tawagar Mali, ya rike wasu kungiyoyin Faransa da ke buga karamar gasar kasar.

Chelle, mai shekara 47 ya samu kwarewa a aikin horarwa ne a kungiyoyin GS Consolat, FC Martigues, MC Oran and Boulogne kuma a shekarar 2022 ce Mali ta nada shi a matsayin wanda zai jagoranci babbar tawagar kasar, kuma ya bayar da mamaki bayan ya kai kasar gasar cin Kofin Afirka ta 2023 da aka gudanar a Ibory Coast inda a gasar ce, Mali ta samu nasarar kai wa matakin kwata-fainal, kafin mai masaukin baki ta fitar da ita a karin lokaci, sai dai bayan gasar ne kasar ta kore shi a watan Yunin 2024.

Labarai Masu Nasaba

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

‘Rike Super Eagle ba karamin aiki ba ne’

Amma kuma aikin horar da Nijeriya babban aiki ne da ke bukatar kwarewa da jajircewar koci, la’akari da yadda kasar nan ke da fitattun ‘yan wasa da ke buga wasa a wasu manyan kungiyoyin Turai wanda hakan yake nufin ko a wajen gayyatar ‘yan wasa akwai babban aiki a wajen mai koyar da tawagar Nigeriya saboda akwai ‘yan wasa da yawa kuma suna kokarin da ya kamata a gayyace su.

To amma duk da kwararrun ‘yan wasa da kasar nan ke da su, tana fama da matsalar samun nasarorin da ake bukata a wasanninta, musamman a Afirka kuma mutane da alama na alakanta rashin katabus da Super Eagle ke yi da rashin kwararren koci, wanda zai iya hada fitattun ‘yanwasan da kasar ke da su domin hada tawaga mai karfin da za ta lashe babbar gasa.

Masu koyarwa da dama – na ciki da wajen kasar nan sun zo, sun kuma tafi, amma babbar tambayar da ke yawo a bakunan ‘yan Nigeriya, shi ne shin

Eric Chelle zai iya fitar wa Super Eagles kitse daga wuta?

Cikin sanarwar nadin nasa, NFF ta dora masa alhakin kai Nijeriya gasar Kofin Duniya domin a yanzu haka kasar nan na matsayi na biyar a kan teburin neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026 da maki uku, bayan da ta ji jiki a hannun Benin da Lesotho sannan wasannin farko da Chelle zai fuskanta a neman gurbin Gasar Kofin Duniya ta 2026 su ne a watan Maris inda zai buga wasanni biyu. Amma kuma a yanzu hankula sun koma kan sabon kocin domin ganin irin rawar da zai taka wajen farfado da Super Eagles.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Eric ChelleKociSuper EaglesWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Matasa Masu Kananan Shekaru Ke Zuwa Neman Aurena Na Matukar Daure Min Kai -Hadizan Saima

Next Post

Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

Related

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

2 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

2 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

3 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

5 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

5 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

5 days ago
Next Post
Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.