• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Éric Sékou Chelle: Sabon Kociyan Super Eagles

by Abba Ibrahim Wada
8 months ago
in Wasanni
0
Éric Sékou Chelle: Sabon Kociyan Super Eagles
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A satin da ya gabata ne hukumar kwallon kafar Nijeriya, NFF ta tabbatar da daukar Éric Sékou Chelle a matsayin sabon kocin kungiyar kwallan kafa ta Super Eagles kuma kamar yadda sanarwar ta tabbatar nadin Chelle ya fara aiki ne nan take inda a cewar hukumar NFF ta yanke shawarar daukar sabon kocin ne daga ketare a zaman da ta yi ranar 2 ga watan Janairun wannan shekarar ta 2025.

NFF ta ce babban aikin da ta dora wa tsohon kocin dan asalin kasar Mali shi ne: kai Nijeriya Gasar Kofin Duniya ta 2026, abin da masana kwallon kafa a nahiyar Afirka da ma Nigeriya suke ganin da kamar wuya ganin yadda rukunin da Nigeriya take ciki yake da kuma kalubalen da ke gaban samun tikitin zuwa gasar ta cin kofin duniya da zai fara jagorantar Nigeriya a cikin wannan shekarar.

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Waye Éric Sékou Chelle

Ba kamar sauran fitattu a harkar kwallon kafar Afirka, irin su George Weah da Abedi Pele da Samuel Eto’o da Rashidi Yekini da sauransu ba, Eric Chelle ba fitacce ba ne a kwallon kafar Afirka, dalili kuwa shi ne a lokacin da yake dan wasa bai wani shahara sosai ba saboda a lokacin da yake buga wasa, sau biyar kawai ya buga wa babbar tagawar kwallon kwallon kafar kasarsa, Mali wasa. Dangane da matakin kungiyoyi kuwa, ya buga wasa ne yawanci a kananan kungiyoyin Faransa, irin su Martigues da Balenciennes da Lens da Istres da kuma Chamois Niortais. To sai dai Chelle ya bai wa mutane da dama mamaki a matakin koci saboda irin kokarin da ake ganin ya yi domin kafin ya zama kocin babbar tawagar Mali, ya rike wasu kungiyoyin Faransa da ke buga karamar gasar kasar.

Chelle, mai shekara 47 ya samu kwarewa a aikin horarwa ne a kungiyoyin GS Consolat, FC Martigues, MC Oran and Boulogne kuma a shekarar 2022 ce Mali ta nada shi a matsayin wanda zai jagoranci babbar tawagar kasar, kuma ya bayar da mamaki bayan ya kai kasar gasar cin Kofin Afirka ta 2023 da aka gudanar a Ibory Coast inda a gasar ce, Mali ta samu nasarar kai wa matakin kwata-fainal, kafin mai masaukin baki ta fitar da ita a karin lokaci, sai dai bayan gasar ne kasar ta kore shi a watan Yunin 2024.

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

‘Rike Super Eagle ba karamin aiki ba ne’

Amma kuma aikin horar da Nijeriya babban aiki ne da ke bukatar kwarewa da jajircewar koci, la’akari da yadda kasar nan ke da fitattun ‘yan wasa da ke buga wasa a wasu manyan kungiyoyin Turai wanda hakan yake nufin ko a wajen gayyatar ‘yan wasa akwai babban aiki a wajen mai koyar da tawagar Nigeriya saboda akwai ‘yan wasa da yawa kuma suna kokarin da ya kamata a gayyace su.

To amma duk da kwararrun ‘yan wasa da kasar nan ke da su, tana fama da matsalar samun nasarorin da ake bukata a wasanninta, musamman a Afirka kuma mutane da alama na alakanta rashin katabus da Super Eagle ke yi da rashin kwararren koci, wanda zai iya hada fitattun ‘yanwasan da kasar ke da su domin hada tawaga mai karfin da za ta lashe babbar gasa.

Masu koyarwa da dama – na ciki da wajen kasar nan sun zo, sun kuma tafi, amma babbar tambayar da ke yawo a bakunan ‘yan Nigeriya, shi ne shin

Eric Chelle zai iya fitar wa Super Eagles kitse daga wuta?

Cikin sanarwar nadin nasa, NFF ta dora masa alhakin kai Nijeriya gasar Kofin Duniya domin a yanzu haka kasar nan na matsayi na biyar a kan teburin neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026 da maki uku, bayan da ta ji jiki a hannun Benin da Lesotho sannan wasannin farko da Chelle zai fuskanta a neman gurbin Gasar Kofin Duniya ta 2026 su ne a watan Maris inda zai buga wasanni biyu. Amma kuma a yanzu hankula sun koma kan sabon kocin domin ganin irin rawar da zai taka wajen farfado da Super Eagles.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Eric ChelleKociSuper EaglesWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Matasa Masu Kananan Shekaru Ke Zuwa Neman Aurena Na Matukar Daure Min Kai -Hadizan Saima

Next Post

Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

4 hours ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

3 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

3 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

5 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

5 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

6 days ago
Next Post
Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.