• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

by Sadiq
2 days ago
in Manyan Labarai
0
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyoyi da ƙasashen duniya sun yi jimami da ta’aziyyar rasuwar tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti da ke birnin Landan a ranar Lahadi, kuma aka binne shi a ranar Talata a garinsu Daura, Jihar Katsina.

Ofishin Tarayyar Turai (EU) a Nujeriya ya wallafa saƙon ta’aziyyarsa a kafar sada zumunta.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
  • Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

EU ta yaba wa Buhari bisa shekara takwas da ya yi yana shugabancin Nijeriya, inda ta ce yana da kishin haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da bin doka a harkokin duniya.

“EU na miƙa ta’aziyyarta ta musamman ga al’ummar Nijeriya bisa rasuwar tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. A lokacin mulkinsa, Buhari ya nuna goyon baya ga haɗin gwiwa da kuma tsarin dokokin duniya,” in ji sanarwar.

Haka kuma, ofishin jakadancin Turkiyya a Abuja ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

Jakadan Turkiyya a Nijeriya, Mehmet Poroy, ya yi masa addu’a domin samun rahamar Allah.

Tun da farko, Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya ya fitar da sanarwa a shafinsa X, inda ya miƙa ta’aziyya ga ’yan Nijeriya bisa rasuwar tsohon shugaban.

Sanarwar ta ce rayuwar Buhari cike ta ke da hidima, ladabi da jajircewa wajen gaskiya a shugabanci.

Gwamnatin ƙasar China ma ta miƙa saƙon ta’aziyyarta ta hannun ofishin jakadancinta da ke Abuja a shafin X a ranar Lahadi.

Sun yaba wa Buhari tare da nuna baƙin ciki game da rasuwarsa.

Sanarwar ta ce: “Ofishin jakadancin ƙasar China a Nijeriya na miƙa ta’aziyyarsa ta musamman ga al’ummar Nijeriya bisa rasuwar tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariEURasuwaTurkiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Next Post

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

Related

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

7 hours ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

10 hours ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

13 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

17 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

19 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

21 hours ago
Next Post
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

July 17, 2025
Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar Ɗantata

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar Ɗantata

July 17, 2025
Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

July 17, 2025
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

July 17, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

July 17, 2025
Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

July 17, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

July 17, 2025
Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

July 17, 2025
Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

July 17, 2025
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.