• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Juna, Ita Ce Tushen Ingantacciyar Dangantaka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Fahimtar Juna, Ita Ce Tushen Ingantacciyar Dangantaka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan ne aka yi bikin bude cibiyar koyar da harshen Sinanci da kamfanin gine-gine na kasar Sin na CRCC ya yi wa kwaskwarima, a makarantar sakandare ta Garki Area 11 dake Abujan Nijeriya.

Haka zalika a jiya, an yi bikin bude kwalejin Confuscious a jami’ar Alkahira dake Masar, don kaddamar da shirin koyar da harshen Sinanci.

  • Shugaban Malawi Ya Jinjinawa Matakin Kasar Sin Na Yafewa Kasashen Afirka Basussuka Marasa Ruwa

Bambancin harshe babban kalubale ne dake karan tsaye ga kusan kowacce mu’amala, sannan fahimtar juna, ita ce tushen ingantacciyar dangantaka da za ta tabbatar da dorewarta.

Muddin aka samu fahimtar juna ta fuskar al’adu da harshe, to za a samu zaman lafiya da ci gaba tsakanin bangarori daban daban. A nan gaba, cikin shekaru kalilan, al’ummomin Sin da Afrika za su dunkule.

Shirye-shiryen na koyar da harshen Sinanci a Nijeriya da Masar, sun shafi makarantu ne na sakandare, wannan kuma ya nuna kaifin basirar Sin na mayar da hankali kan yara manyan gobe.

Labarai Masu Nasaba

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Kamar yadda ake cewa, da zafi-zafi a kan daki karfe, wato fahimtar al’adun Sin da ma harshen Sinanci ga yara a nahiyar Afrika, za ta bayar da gagarumar gudunmawa wajen gina al’ummar Sin da Afrika ta bai daya, kuma mai kyakkyawar makoma.

Wasu za su ce, to shin ita kasar Sin tana koyar da harsunan Afrika a kasarta? Abun burgewa shi ne, kasar ta shafe gomman shekaru tana koyar da harsunan Afrika, har dalibai na samu shaidar digiri a harshen Hausa da sauran wasu harsunan Afrika kamar Kiswahili. Baya ga haka, da idona, na ga wani littafin karatu na daliban ajin firamare, dake dauke da harshen Hausa.

A sannan nan kara fahimtar lallai Sin ta yi nisa a kokarinta na habaka dangantaka da Nijeriya da ma sauran kasashen Afrika.

Ilimi shi ne gishirin rayuwa. Haka kuma kashin bayan ci gaban kowacce al’umma. Yadda gwamnati da kamfanonin kasar Sin ke mayar da hankali wajen bayar da gudunmawa ga kyautatuwar ilimi a Nijeriya da sauran kasashen Afrika, ya cancanci yabo, domin lamari ne da za a ga alfanunsa a nan gaba.

Kamar yadda shugaban hukumar ilimi a matakin farko ta birnin Abuja, Alhassan Sule ya bayyana, daddadiyar dangantakar Sin da Nijeriya ta taimaka sosai ga aikin samar da ilimi a kasar. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’addan ISWAP Da Dama A Yobe

Next Post

Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero

Related

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

11 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

12 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

13 hours ago
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

15 hours ago
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

16 hours ago
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

17 hours ago
Next Post
Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero

Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero

LABARAI MASU NASABA

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.