• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Manufofin Nijeriya A Kasashen Waje A Karkashin Tuggar

by Bello Hamza
6 months ago
in Bakon Marubuci
0
Fahimtar Manufofin Nijeriya A Kasashen Waje A Karkashin Tuggar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babu wani abu da ya gwada irin tsayin daka kan manufofin harkokin wajen Nijeriya a tsawon shekara 67 da kuma kwarewa, hangen nesa da kuma fahimtar manufofin Nijeriya daga ministan harkokin waje, Yusuf Maitama Tuggar, kamar sauyin gwamnati da aka yi a jamhuriyar Nijar ba bisa ka’ida ba, da kafa kungiyar kawancen kasashen Sahel, AES, da kuma irin halin tsokanar da gwamnatin mulkin soja take yi wa Nijeriya.

Ba wai bisa hadari ba ne ya sa Nijeriya ta iya daukar matakai wajen iya tafiyar da rikicin diflomasiyya da gwamnatin mulkin sojan Nijar, Burkina Faso da kuma Mali. Tambayar da ya kamata a yi a nan ita ce: mene ne sirrin, kuma mene ne lakanin, da har Nijeriya ta yi na magance matakan bata suna, barazana da kuma farfaganda na AES?

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Ana iya samun wannan amsar a cikin rubutun da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya yi mai taken “Manufar Harkokin Waje da Hanyar Zaman Lafiya Da Makwabciya Mai Hatsari”. Wannan rubutun zai bube ido ga duk mai sha’awar fahimtar manufofin Nijeriya a kasashen waje.

Daya daga cikin manufofin shi ne – “Habaka dokokin kasa da kasa da wajibcin yarjejeniya”. A sakamakon haka matakin da Nijeriya ta dauka wajen kakaba wa gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar takunkumi ya kasance a karkashin wannan manufa.

Ministan ya yi taka-tsan-tsan wajen tunatar da mu cewa: “Tsarin mulki (kuma) ya bayyana dalilin da ya sa duk wata gwamnatin Nijeriya da ke da iko za ta damu matuka idan makwabciyarta ta kasance tana gudanar da mulki ba tare da kundin tsarin mulki ko ka’ida ba”. Abin da hakan ke nufi shi ne, a tsarin mulki, ya zama wajibi Nijeriya a matsayinta na memba a kungiyar ECOWAS ta mutunta tare da inganta yarjejeniyoyin ECOWAS da ka’idoji da sauran dokokin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Babban sakon ministar shi ne cewa manufofin harkokin waje na Nijeriya sun ginu ne a kan tsarin mulki da bin doka da oda. A yayin da Nijeriya ke mutunta ka’idojin zirga-zirgar al’umma na ECOWAS, Jamhuriyyar Nijar, a shekarar 2015, alal misali, ta je ta ayyana wata doka kan ‘yan ci-rani da ta saba wa ka’ida. Shin wannan bai isa ba ya nuna wane ne yake mutunta doka ba?, da kuma wane ne wanda ba ya mutunta doka?

Dangane da yadda ake amfani da diflomasiyya da sauran hanyoyin da dimokuradiyya ta tanada, ministan ya bayyana a cikin rubutunsa, irin abubuwan da gwamnati ta yi na magance batutuwan da suka shafi mulkin sojan Nijar da sauran membobin kungiyar AES.

Amma duk da haka wasu masu suka na ci gaba da tabbatar da taurin kai da rashin hadin kai daga gwamnatin mulkin soja kan takunkumin da aka kakaba wa masu satar mulki. A lokaci guda kuma, wadannan masu suka da tada jijiyar wuya sun ki amincewa da irin matakan lallami da hankali da aka nuna wa masu mulkin sojan.

Wani muhimmin batu na rubutun ministan shi ne “Tsarin cin gashin kai” a matsayin ginshiki na manufofin gwamnatin Tinubu. Nijeriya na da hakki da ‘yanci, kuma tana da hakkin yin hulda da kowacce kasa ba tare da wani ya fada mata, ko ya jagorance ta ko umurtar ta ba. Dole ne Nijeriya ta yi aiki tare da gabas da yamma, da dukkan manyan kasashe. Nijeriya ba ta nuna wariya a manufofinta na kasashen waje. Jamhuriyar Nijar, ko wata kasa ba za ta zayyana mana kasashen da za mu yi hulda da su ba.

Habaka hadin kan Afirka da goyon bayan hadin kan Afirka ya kasance wani abu muhimmi kuma na dindindin a manufofin harkokin waje na Nijeriya kamar yadda ministan ya bayyana. Nijeriya memba ce ta ECOWAS da AU – kuma dukkanninsu suna aiki ba dare ba rana domin ganin an samu hadin kai, ta hanyar amfani da tsarin bi a hankali kuma mataki-mataki.

Abu mafi muhimmanci, ministan ya kuma tunatar da wadanda suke yada zarge-zarge marasa tushe balle makama a kan Nijeriya da cewa “A halin yanzu Nijeriya na da sojoji a ayyukan wanzar da zaman lafiya a Guinea Bissau da Gambia. Nijeriya kuma ita ce ke kan gaba wajen tabbatar da rundunar ECOWAS a matsayin masu jiran ko ta kwana, duka wannan a kokarinta na yaki da ta’addanci da rashin zaman lafiya a yankinmu a karkashin doka”.

  • Kwamared Bishir Dauda, Sabuwar Unguwa Katsina.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EASMakamashiNijeriyaTuggar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴansanda A Gombe Sun Yi Holar Masu Laifuka

Next Post

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

Related

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

2 weeks ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

3 weeks ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

1 month ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

2 months ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

2 months ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

3 months ago
Next Post
Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.