ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Manufofin Nijeriya A Kasashen Waje A Karkashin Tuggar

by Bello Hamza
1 year ago
Tuggar

Babu wani abu da ya gwada irin tsayin daka kan manufofin harkokin wajen Nijeriya a tsawon shekara 67 da kuma kwarewa, hangen nesa da kuma fahimtar manufofin Nijeriya daga ministan harkokin waje, Yusuf Maitama Tuggar, kamar sauyin gwamnati da aka yi a jamhuriyar Nijar ba bisa ka’ida ba, da kafa kungiyar kawancen kasashen Sahel, AES, da kuma irin halin tsokanar da gwamnatin mulkin soja take yi wa Nijeriya.

Ba wai bisa hadari ba ne ya sa Nijeriya ta iya daukar matakai wajen iya tafiyar da rikicin diflomasiyya da gwamnatin mulkin sojan Nijar, Burkina Faso da kuma Mali. Tambayar da ya kamata a yi a nan ita ce: mene ne sirrin, kuma mene ne lakanin, da har Nijeriya ta yi na magance matakan bata suna, barazana da kuma farfaganda na AES?

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Ana iya samun wannan amsar a cikin rubutun da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya yi mai taken “Manufar Harkokin Waje da Hanyar Zaman Lafiya Da Makwabciya Mai Hatsari”. Wannan rubutun zai bube ido ga duk mai sha’awar fahimtar manufofin Nijeriya a kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin manufofin shi ne – “Habaka dokokin kasa da kasa da wajibcin yarjejeniya”. A sakamakon haka matakin da Nijeriya ta dauka wajen kakaba wa gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar takunkumi ya kasance a karkashin wannan manufa.

Ministan ya yi taka-tsan-tsan wajen tunatar da mu cewa: “Tsarin mulki (kuma) ya bayyana dalilin da ya sa duk wata gwamnatin Nijeriya da ke da iko za ta damu matuka idan makwabciyarta ta kasance tana gudanar da mulki ba tare da kundin tsarin mulki ko ka’ida ba”. Abin da hakan ke nufi shi ne, a tsarin mulki, ya zama wajibi Nijeriya a matsayinta na memba a kungiyar ECOWAS ta mutunta tare da inganta yarjejeniyoyin ECOWAS da ka’idoji da sauran dokokin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

Babban sakon ministar shi ne cewa manufofin harkokin waje na Nijeriya sun ginu ne a kan tsarin mulki da bin doka da oda. A yayin da Nijeriya ke mutunta ka’idojin zirga-zirgar al’umma na ECOWAS, Jamhuriyyar Nijar, a shekarar 2015, alal misali, ta je ta ayyana wata doka kan ‘yan ci-rani da ta saba wa ka’ida. Shin wannan bai isa ba ya nuna wane ne yake mutunta doka ba?, da kuma wane ne wanda ba ya mutunta doka?

Dangane da yadda ake amfani da diflomasiyya da sauran hanyoyin da dimokuradiyya ta tanada, ministan ya bayyana a cikin rubutunsa, irin abubuwan da gwamnati ta yi na magance batutuwan da suka shafi mulkin sojan Nijar da sauran membobin kungiyar AES.

Amma duk da haka wasu masu suka na ci gaba da tabbatar da taurin kai da rashin hadin kai daga gwamnatin mulkin soja kan takunkumin da aka kakaba wa masu satar mulki. A lokaci guda kuma, wadannan masu suka da tada jijiyar wuya sun ki amincewa da irin matakan lallami da hankali da aka nuna wa masu mulkin sojan.

Wani muhimmin batu na rubutun ministan shi ne “Tsarin cin gashin kai” a matsayin ginshiki na manufofin gwamnatin Tinubu. Nijeriya na da hakki da ‘yanci, kuma tana da hakkin yin hulda da kowacce kasa ba tare da wani ya fada mata, ko ya jagorance ta ko umurtar ta ba. Dole ne Nijeriya ta yi aiki tare da gabas da yamma, da dukkan manyan kasashe. Nijeriya ba ta nuna wariya a manufofinta na kasashen waje. Jamhuriyar Nijar, ko wata kasa ba za ta zayyana mana kasashen da za mu yi hulda da su ba.

Habaka hadin kan Afirka da goyon bayan hadin kan Afirka ya kasance wani abu muhimmi kuma na dindindin a manufofin harkokin waje na Nijeriya kamar yadda ministan ya bayyana. Nijeriya memba ce ta ECOWAS da AU – kuma dukkanninsu suna aiki ba dare ba rana domin ganin an samu hadin kai, ta hanyar amfani da tsarin bi a hankali kuma mataki-mataki.

Abu mafi muhimmanci, ministan ya kuma tunatar da wadanda suke yada zarge-zarge marasa tushe balle makama a kan Nijeriya da cewa “A halin yanzu Nijeriya na da sojoji a ayyukan wanzar da zaman lafiya a Guinea Bissau da Gambia. Nijeriya kuma ita ce ke kan gaba wajen tabbatar da rundunar ECOWAS a matsayin masu jiran ko ta kwana, duka wannan a kokarinta na yaki da ta’addanci da rashin zaman lafiya a yankinmu a karkashin doka”.

  • Kwamared Bishir Dauda, Sabuwar Unguwa Katsina.
Tuggar
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
obi
Bakon Marubuci

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Bakon Marubuci

Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya

May 10, 2026
Next Post
Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.