ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Manufofin Nijeriya A Kasashen Waje A Karkashin Tuggar

by Bello Hamza
1 year ago
Tuggar

Babu wani abu da ya gwada irin tsayin daka kan manufofin harkokin wajen Nijeriya a tsawon shekara 67 da kuma kwarewa, hangen nesa da kuma fahimtar manufofin Nijeriya daga ministan harkokin waje, Yusuf Maitama Tuggar, kamar sauyin gwamnati da aka yi a jamhuriyar Nijar ba bisa ka’ida ba, da kafa kungiyar kawancen kasashen Sahel, AES, da kuma irin halin tsokanar da gwamnatin mulkin soja take yi wa Nijeriya.

Ba wai bisa hadari ba ne ya sa Nijeriya ta iya daukar matakai wajen iya tafiyar da rikicin diflomasiyya da gwamnatin mulkin sojan Nijar, Burkina Faso da kuma Mali. Tambayar da ya kamata a yi a nan ita ce: mene ne sirrin, kuma mene ne lakanin, da har Nijeriya ta yi na magance matakan bata suna, barazana da kuma farfaganda na AES?

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Ana iya samun wannan amsar a cikin rubutun da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya yi mai taken “Manufar Harkokin Waje da Hanyar Zaman Lafiya Da Makwabciya Mai Hatsari”. Wannan rubutun zai bube ido ga duk mai sha’awar fahimtar manufofin Nijeriya a kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin manufofin shi ne – “Habaka dokokin kasa da kasa da wajibcin yarjejeniya”. A sakamakon haka matakin da Nijeriya ta dauka wajen kakaba wa gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar takunkumi ya kasance a karkashin wannan manufa.

Ministan ya yi taka-tsan-tsan wajen tunatar da mu cewa: “Tsarin mulki (kuma) ya bayyana dalilin da ya sa duk wata gwamnatin Nijeriya da ke da iko za ta damu matuka idan makwabciyarta ta kasance tana gudanar da mulki ba tare da kundin tsarin mulki ko ka’ida ba”. Abin da hakan ke nufi shi ne, a tsarin mulki, ya zama wajibi Nijeriya a matsayinta na memba a kungiyar ECOWAS ta mutunta tare da inganta yarjejeniyoyin ECOWAS da ka’idoji da sauran dokokin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

Babban sakon ministar shi ne cewa manufofin harkokin waje na Nijeriya sun ginu ne a kan tsarin mulki da bin doka da oda. A yayin da Nijeriya ke mutunta ka’idojin zirga-zirgar al’umma na ECOWAS, Jamhuriyyar Nijar, a shekarar 2015, alal misali, ta je ta ayyana wata doka kan ‘yan ci-rani da ta saba wa ka’ida. Shin wannan bai isa ba ya nuna wane ne yake mutunta doka ba?, da kuma wane ne wanda ba ya mutunta doka?

Dangane da yadda ake amfani da diflomasiyya da sauran hanyoyin da dimokuradiyya ta tanada, ministan ya bayyana a cikin rubutunsa, irin abubuwan da gwamnati ta yi na magance batutuwan da suka shafi mulkin sojan Nijar da sauran membobin kungiyar AES.

Amma duk da haka wasu masu suka na ci gaba da tabbatar da taurin kai da rashin hadin kai daga gwamnatin mulkin soja kan takunkumin da aka kakaba wa masu satar mulki. A lokaci guda kuma, wadannan masu suka da tada jijiyar wuya sun ki amincewa da irin matakan lallami da hankali da aka nuna wa masu mulkin sojan.

Wani muhimmin batu na rubutun ministan shi ne “Tsarin cin gashin kai” a matsayin ginshiki na manufofin gwamnatin Tinubu. Nijeriya na da hakki da ‘yanci, kuma tana da hakkin yin hulda da kowacce kasa ba tare da wani ya fada mata, ko ya jagorance ta ko umurtar ta ba. Dole ne Nijeriya ta yi aiki tare da gabas da yamma, da dukkan manyan kasashe. Nijeriya ba ta nuna wariya a manufofinta na kasashen waje. Jamhuriyar Nijar, ko wata kasa ba za ta zayyana mana kasashen da za mu yi hulda da su ba.

Habaka hadin kan Afirka da goyon bayan hadin kan Afirka ya kasance wani abu muhimmi kuma na dindindin a manufofin harkokin waje na Nijeriya kamar yadda ministan ya bayyana. Nijeriya memba ce ta ECOWAS da AU – kuma dukkanninsu suna aiki ba dare ba rana domin ganin an samu hadin kai, ta hanyar amfani da tsarin bi a hankali kuma mataki-mataki.

Abu mafi muhimmanci, ministan ya kuma tunatar da wadanda suke yada zarge-zarge marasa tushe balle makama a kan Nijeriya da cewa “A halin yanzu Nijeriya na da sojoji a ayyukan wanzar da zaman lafiya a Guinea Bissau da Gambia. Nijeriya kuma ita ce ke kan gaba wajen tabbatar da rundunar ECOWAS a matsayin masu jiran ko ta kwana, duka wannan a kokarinta na yaki da ta’addanci da rashin zaman lafiya a yankinmu a karkashin doka”.

  • Kwamared Bishir Dauda, Sabuwar Unguwa Katsina.
Tuggar
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Next Post
Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Saukake (2)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.