• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]

by Nuhu Ubale Ibrahim
7 months ago
in Addini, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ibu Juzai al-Kalbi Allah ya yi masa rahama ya ce:

“يُؤْمَرُ الْقَارِئُ بِالِاسْتِعَاذَةِ قَبْلَ الْقِرَاءَةِ”

Fassara:

“Ana umurtar mai karatu da yin isti’aza kafin ya fara karatun Alƙur’ani”

Fashin Baƙi:

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Wannan umurni yana da tushen shari’a daga Alƙur’ani da Hadisi, kuma yana da hikima da fa’ida da dama. Allah Ta’ala Ya umurci Musulumi da yin isti’aza kafin karanta Alƙur’ani kamar yadda Ya labarta mana haka a cikin Suratul Nahli a aya ta 98. Inda Ya ce:” To idan za ka karanta Alƙur’ani sai ka nemi tsarin Allah daga Shaiɗan korarre (daga rahamar Allah).” Wannan aya ta tabbatar da neman tsarin Allah kafin a fara karatun Alƙur’ani.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [3]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Ma’anar Isti’aza:

Isti’aza na nufin neman tsari da kariya da fake wa a wurin Allah Shi kaɗai ban da waninsa daga sharrin Shaiɗan. Domin ƙarin haske duba Ibnu Jarir; Jãmi’ul Bayãni [1/111], Ibnu Kasir; Tafsirul Kur’anil Azim [1/27], da Ibnul Ƙayyim; Badã’i’ul Fawã’id [2/200].

Yaushe ake Isti‘aza?:
Malamai sun yi saɓani dangane da lokacinda za a yi Isti‘aza, sai dai magana mafi ingani da malamai mafiya yawa suke a kanta shi ne ana yin Isti‘aza ne kafin a fara karatu. Domin ƙarin haske duba Ibnu Ibnu Juzai; Kitãbut Tashīl fi Ulūmil Kitãbi [1/30], da Bagawī; Ma’ãlumut Tanzīli [[5/42] da Ibnu Aɗiyya; al-Muharrul Wajizi [1/58], da Ibnul Jauzi; Zãdul Masīri [1/14].

Hukunci Isti‘aza Kafin Karanta Alƙur’ani:

Malamai mafiya yawa sun tafi a kan mustahabbi ne yin isti‘aza a lokacin karanta Alƙur’ani a wajen salla. Amma sun yi saɓani a wajen karatun salla, an hakaitu Imamu Malik ba ya isti‘aza a sallar farilla amma yana yi a sallar asham, shi sa ake yi a sallar nafila. Amma Imam Abu Hanifa da Imam Asshafi’i suna yi isti‘aza a sallar farilla. Akwai waɗanda suke ganin wajibi ne a yi isti‘aza a salla gaba ɗaya. Domin ƙarin haske duba Kitãbu at-Tashīlu fi Ulūmi at-Tanzil [1/30] da Ibnu Kasir; Tafsirul Kur’anil Azim [1/26] da al-Ƙurɗubi; al-Jãmi’u Li’ahkãmil Ƙur’ãni [1/86]

Hikimar Yin Isti’aza Kafin Karanta Alƙur’ani:

Akwai hikimomi masu tarin yaw na yin isti‘aza kafin karatu. Ga wasu daga cikinsu:

1. Kariya daga tasirin Shaiɗan: Shaiɗan yana hana mutum fahimtar Alƙur’ani kuma yana kuma sanya ruɗani. Yin isti’aza na kare mai karatu daga fitinarsa.

2. Tsaftace zuciya: Isti’aza kafin karanta karanta Alƙur’ani yana ba wa zuciya tsarki da nufin Allah a karatu da samin tsoron Allah, tare da tadabburi.

3. Bin sunnon Annabi (SAW): Domin Annabi (SAW) yana Isti’aza kafin ya fara karatu.

4. Tsaftace Baki: Yin isti‘aza yana tsaftace baki daga abuwan da ta aikata na wargi da yasasshen zance, domin shiga karanta maganar Allah cikin tsarki da tsafta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafawa Duniya Gwiwa Ta Hanyar Fadada Bude Kofar Ta

Next Post

Sabon Kwamishinan ‘Yansanda Ya Kama Aiki A Kano

Related

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

1 day ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 weeks ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 weeks ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

4 weeks ago
Next Post
Sabon Kwamishinan ‘Yansanda Ya Kama Aiki A Kano

Sabon Kwamishinan ‘Yansanda Ya Kama Aiki A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.