• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shahararren Lauya mai rajin kare hakkin Dan Adam Femi Falana ya kai karar Gwamnatocin tarayya dana Jihohi 36 kotu da sauran masu fada aji ta bangaren ilimi, a kan irin halin da yaran da basu zuwa makaranta suke ciki.

Karar wadda babban lauya kasa tare da abokiyarsa tun suna ‘yan yara kwararriya ce ta bangaren ilimi Hauwa Mustapha,a madadin kungiyar ‘Alliance on Surbibing COBID-19’ da ta hada tare da Ministan ilimi da hukumar kula da ilimin bai daya suna daga cikin wadanda aka yi karar.

  • Kayayyaki Kirar Kasar Sin Na Samun Karbuwa Sosai A Kasashen Ketare
  • Kun Kasa Magana A Lokacin Buhari, Ba Ku Da Damar Sukar Tinubu – Matasan Arewa

Babban mai shari’a na kasa tare da manyan masu shari’a na Jihohi, Ministan Babban birnin tarayya Abuja suna daga cikin wadanda aka yi karar,an shiga da karar ne ta hannun Lauyarsu Mrs Funmi Falana (SAN).
Karar tana magana ne kan zargin da ake yi yadda aka kasa amfani da Naira bilyan 68 kudaden da aka warewa hukumar saboda samar da ilimi kyauta ga kowane yaro a Nijeriya.

Falana yana so ne wadanda aka yi karar da suka hada da gwamnatin tarayya, ma’ikatar ilimi hukumar ilimin bai daya, da dukkan Jihohi 36 saboda alhakin samar da ilimi kyauta ga dukkan yara wadanda suka isa shiga makaranta ya rataya a kansu ne.

Koda yake dai shi al’amarin yara wadanda basu zuwa makaranta wadanda ake sa ran sun kai miliyan 20 da dubu 200,000 idan aka yi la’akari da rahoton UNICEF da ba’a dade da fitarwa ba shi yasa aka dauki matakin zuwa kotun.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Karar an shigar da ita ne ranar 19 ga Janairu na shekarar 2024 a kotun tarayya da ke Legas inda aka bukaci kotun da ta yi bayani akan tuhumar wadanda aka kai karar.

“Ana dai son a gane ko wadanda aka kai karar alhakin samar da ilimin bai daya a dole, kuma kyauta ga kowane yaro dan asalin Nijeriya da ya kai shekarun shiga makaranta,kamar yadda sashe na 2 karamin sashe na (1) dokar da ta bada damar samar da ilimi dole kuma kyauta mai namba, LFN, 2004.

“Ko rashin yin aiki yadda doka ta bada dama ga wadanda aka yi karar su bada abin da bai gaza kashi 50 kudaden ayyukan da za ayi da hakan zai nuna suma sun nuna suna bayan ba kowane yaro dan Nijeriya ilimi kyauta abin da dole ne sai hakan ta kasance, a matsayin sun yi na’ama da lamarin.Ba karamin laifi bane wajen kin yin amfani ga dokar data bada dama wajen samar da ilimin bai daya kyauta kamar yadda dokar shekarar 2004 ta ilimi ta tanadar.

A karar da Femi Falana ya shigar akotun tarayya Legas ranar 26 ga watan Janairu 2024, babban lauyan yace rahoto ya fitar da shi wanda hukumar kula da al’amuran gaggawa na kananan yara karkashin majalisar dinkin duniya bada dadewa bane aka kiyasta da akwai yara a Nijeriya da suka kai milyan 20.2 da basu zuwa makaranta.
Falana ya ce rahoton ya nuna daya daga cikin yara uku ‘yan Nijeriya baya zuwa makaranta,bugu da kari kuma kasar ita tafi yawan yara wadanda basu zuwa makaranta a duniya.

Ya ce “Wanda aka yi karar na farko shi ne Ministan shari’a shi ne kuma na farko mai kula ana tursasa bin doka kamar yadda kotunan Nijeriya suka bukaci da ayi hakan.
“Wanda aka yi kara na biyu tsarin Mulki ya bashi damar aiwatar da tsare-tsaren ilimi a kowane bangare na ilimi cikin inganci a Nijeriya.

“Cikin jerin wadanda ake kara hukumar kula da ilimin bai daya shi ke da alhakin rabawa Jihohi kudade da sauran masu ruwa da tsaki da jagorancin aiwatar da tsarin hukumar a illahirin Nijeriya.

“Na 4 zuwa 40 sun hada da wadanda suke lura da al’amuran shari’a na Jihohi 36 na fadin Nijeriya.

“Cewar dokar data kafa hukumar ilimin bai daya da wasu abubuwa da aka kafa, 2004 (UBEA) tana samar da ilimi da ya zama dole ga dukkan yara ‘yan Nijeriya da suka kai shekarun shiga makarantar Firamare da karamar Sakandare a Nijeriya.”
Wadanda suka shigar da karar suna bukatar kotun da ta tilasta yin wadannan abubuwan saboda adalci.

Kamar yadda sashe na 2 karamin sashe na(1)bada dama ta dole a samar da ilmin Firamare da karamar Sakandare kyauta kamar yadda dokar ilimi da dokokin Nijeriya na shekarar 2004,wadanda ake karar doka ta basu damar bada ilimi kyauta da yake dole ga yara wadanda suka kai shekarar shiga makarantar Firamare da karamar Sakandare
Sashe na 11 karamin sashe na(1)ya bada dama ta samar da ilimi daga Firamare zuwa karamar Sakanadare kyauta wanda doka ta bada na cewar gwamnatin tarayya zata rika bada kashi wanda bai kasa da kashi 2 ba na kudaden shigar da take samu a gidauniyar ta ilimi kowace shekara.

Hakanan ma dokar ta sashe na 11 karamin sashe(2)na samar da ilimin Firamare zuwa karamar Sakandare kyauta Jihohi ma ana son kowace Jiha ta samar da abin da bai gaza kashi 50 ba na yawan kudaden da za a kashe na ayyukan da za ayi,kafin ta samu cancantar samun tallafin na gwamnatin tarayya a karkashin karamin sashe na 1(1) na sashen.

Hakanan ma idan aka samu kin amincewa ko su wadanda ake karar suka kasa samun Naira bilyan 68 na ilimin Firamare da karamar Sakandare na yara wadanda suka kai shekarar shigaa Nijeriya, abin da bai dace bane kuma ya sabawa sashe na 1 karamin sashe na dokar samar ilimi da ta zama dole ayi amfani da ita (2).

Akwai doka da ke ba da umarni na na wadanda ake karar daga na 4 zuwa na 40 su biya na su kason kafin su samu damar yin amfani da Naira bilyan 68 daga cikin asusun ajiya na ilmin bai daya da rahoton bin umarni cikin kwana30 lokacin da kotu zata yanke hukunci.

Akwai doka da take umarni wadanda aka yi kara na 4 zuwa na 40 su biya nasu kason domin su samu damar yin amfani da kudaden da aka ware na samar da ilimin bai daya, idan lokacin yin hakan ya yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Babur Da Kasar Sin Ta Samar Yake Samun Karbuwa

Next Post

Za Mu Tabbatar Kotu Ta Hukunta Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa Hudu Ari – Fintiri

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

10 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

12 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

14 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

14 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

17 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

19 hours ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Kotu Ta Hukunta Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa Hudu Ari – Fintiri

Za Mu Tabbatar Kotu Ta Hukunta Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa Hudu Ari - Fintiri

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.