ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kun Kasa Magana A Lokacin Buhari, Ba Ku Da Damar Sukar Tinubu – Matasan Arewa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Matasan Arewa

Kungiyar Matasan Arewa maso yamma ta nuna rashin dacewar kalaman kungiyar dattawan Katsina da suka bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya canza matakan da Gwamnatinsa ta dauka ko kuma ya rasa goyon bayan yankin a zaben 2027. 

Ko’odinetan kungiyar, Alhaji Murtala Aliyu Ka’oje ne ya bayyana hakan a taron manema labarai da suka gudanar a Sakkwato a ranar Litinin inda ya ce, ko kadan dattawan Katsina ba su da kowace irin damar kalubalantar ko wane irin matakin da gwamnatin da ke kan mulki ta dauka saboda a baya sun kasa kalubalantar matakan da ba daidai ba a mulkin Shugaba Muhammadu Buhari.

  • Cire Tallafin Fetur: Ma’aikatan Jihar Jigawa Sun Ki Amincewa Da Karin Albashin Naira 10,000
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Mata Na Gudanar Da Zanga-zanga Kan Tsananin Yunwa Da Tsadar Rayuwa A Neja

Ka’oje ya bayyana cewar duk da yawaitar asarar rayuka da dukiyoyi da tabarbarewar tattalin arzikin Arewa, babu wani dattijon Arewa daga Katsina da ya fito ya yi magana kan gurbatattun manufofin da tsohuwar gwamnati ta dauka wadanda suka illata Arewa da ‘yan Arewa.

ADVERTISEMENT

Kungiyar datawan Katsina dai ta fito fili ta nuna rashin dacewar daukar wasu matakan gwamnati musamman dauke wasu muhimman sassan Babban Bankin Kasa da hukumar kula da filayen jiragen sama daga Abuja zuwa Lagas da kuma aikin fadada filin jirgin sama na Umaru Musa ‘Yar’Adua da ke Katsina.

“Duk da tsananin talauci, matsalolin tsaro da gallazawar siyasa da aka fuskanta a zamanin mulkin Buhari, dattawan Katsina ba su kalubalanci tsohuwar gwamnatin ba?

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“Wata tambayar ita ce, yaushe ne dattawan Katsina suka zama masu sukar manufofin gwamnatin Tarayya? Mutane da dama sun rasa rayuka da dukiyoyi, sha’anin noma ya tsaya cik kamar yadda dukkanin al’amurran rayuwar al’umma suka tabarbare saboda rashin tsaro da rashin iya jagorancin Buhari amma dattawan Katsina ba su taba nuna damuwar gyara lamurran ba?”

Kungiyar ta ce ta na goyon bayan kalaman Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle da ya ce wa dattawan Katsina da sauran kungiyoyi irin nasu da su ba da himma ga hadin kan kasa, su dakatar da kokarin zazafa siyasa ta hanyar kalaman da ba su dace kan Shugaba Tinubu ba.

Matasan Arewa
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    2027:Cece-kuce Ta Barke Tsakanin Tinubu Da Atiku
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Yadda Rikici Ya Tsananta Tsakanin Dan Daba Da Malaman Addini A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dalilin Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Yankin Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Atiku Ya Koka Kan Ƙaruwar Ta’addanci A Sakkwato

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa ‘Yan’uwansa

Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa 'Yan'uwansa

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.