• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni, Siyasa
0
Fara Yakin Neman Zaben APC: Wacce Alkibla Tinubu Ya Dosa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata ce, jam’iyya mai mulki ta APC ta fara gudanar da yakin neman zabenta a garin Jos Babbar Birnin Jihar Filato, domin tallata jam’iyyar ta yadda ‘yan Nijeriya za su sake zabenta a 2023.

Kamar yadda yakin neman zaben 2023 ya kankama, hankulan jam’iyyun siyasa da masu neman takara ya kamo kan tallata manufofinsu a kakafen sadarwa ta yadda za su saye zuciyar masu jefa kuri’a har ma su zabe su.

  • Masu Cutar Sikari Na Fuskantar Karin Kudin Magani Da Kashi 200
  • Da Dumi-Duminsa: Buhari Ya Tsige Fadah A Matsayin Darakta Janar Na NYSC

Sashe na 94 (1) na dokar zaben 2022 ya bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daman dage takunkumin yakin neman zabe tun a ranar 28 ga watan Satumbar 2022.

Bisa tsarin dokar zaben 2022, wannan shi ne karo na farko da kasar nan ta samu damar gudanar da yakin neman zabe har na tsawon watanni biyar, inda a baya ayyukan jam’iyyun siyasa na gudanar da yakin neman zabe ya yi karanci.

Kafin dai hukumar INEC ta dage takunkumin fara yakin neman zabe, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da sauran wasu gwamnoni da ke cikin jam’iyyar sun yi zawarcin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan domin samun goyon bayansa a babban zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Tinubu tare da mataimakin takararsa, Sanata Kashim Shettima da gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun da AbdulRahman AbdulRazak na Jihar Kwara da Bello Matawalle na Jihar Zamfara da gwamnan Jihar Jigawa, Abubakar Badaru da kuma gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong wanda shi ne darakta janar na yakin neman zaben jam’iyyar duk suna daga cikin wadanda suka gana da Jonathan.

Haka kuma tsohon gwamnan Jihar Legas ya ziyarci tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo a Abeokuta da tsofaffin shugabanin kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Babangida da kuma Janar Abdulsalam Abubakar.

Tun da farko dai, jaddawalin ayyukan yakin neman zaben APC an dakatar da su ne bayan da aka samu rudani kan jerin sunayen mambobi 422 na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa.

An dai yi tsammanin cewa jam’iyyar ta samu nasarar dinke barakar wanda aka sake fitar da jerin wadansu sunaye na kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa da kowa ya amince da shi.

Bayan an samu nasarar lallashin ‘ya’yan jam’iyyar da suka fusata, Shugaban Kasa,

Muhammadu Buhari ya kaddamar da kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC tare da amincewa da a zabi Tinubu domin ya gaje shi.

Ya ce zaben Tinubu zai karfafa nasarar da gwamnatinsa ta samu a matsayinsa na dan takara mai nagarta da kyakkyawan shugabanci wanda zai iya dorawa daga wurin da suka tsaya.

Bayan kaddamar da kwamitin yakin neman zaben, an dai samu karancin gudanar da yakin neman zabe a cikin jam’iyya mai mulki wanda ba a yi tsammanin hakan ba. An dai bayyana cewa dalilin da ya sa aka samu tsaikon dai shi ne, mafi yawancin daraktocin yakin neman zaben sun dokara ne da kasafin kudi na gudanar da lamarin. Sannan an bayyana cewa lokacin da aka kammala kasafin kudin, za a saki kudaden ga daraktocin nan take domin gudanar da harkokin yakin neman zabe.

Jam’iyyar APC ta fara gudanar da yakin neman zabenta ne a garin Jos Babban Birnin Jihar Filato a ranar 15 ga watan Nuwamba gabanin zaben 2023. Jam’iyyar ta gana da kungiyoyin manoma a Jihar Neja a ranar 7 ga watan Nuwamba, sannan ta kara wani ganawar irin wannan da kungiyar masu hakar ma’adanai a ranar 9 ga watan Nuwamba a Keffi na Jihar Nasarawa.

Jam’iyya mai mulki ta sake gudanar da irin wannan tattaunawa a Kalaba na Jihar Kuros Ribas a ranar 12 ga watan Nuwamba na yadda za ta fara gudanar da yakin neman zabe a garin Jos ranar 15 ga watan Nuwamba. Wannan yana zuwa ne bayan tattaunawa a Jihar Imo ranar 17, inda daga bisani ta gudanar da ganganminta a Jihar Delta ranar 19 ga watan Nuwamba.

Da yake jawabi a ranar Alhamin da ta gabata lokacin kaddamar da kwamitin tuntuba na yankin arewa maso yamma karkashin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Darakta Hon. Aminu Jaji ya bayyana cewa jam’iyyar ta cancanci yakin neman zabe mai tsari da zai bambanta da na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPPA, Rabi’u Kwankwaso da ke yankin arewa maso yamma.

A cewarsa, wannan lokacin ne da za a saka wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar da kuma mutanen yankin kudu maso yamma bisa yadda suka goyi bayan Shugaban Kasa Buhari a zabukan 2015 da 2019.

Jaji ya ce bisa goyon bayan Shugaba Buhari na tsawan mulkinsa shekara bakwai da rabi, yankin arewa maso yamma zai goyi bayan samun nasarar Tinubu/Shettima a zabe mai zuwa.

Ya dai bukaci mambobin kwamitin yakin neman zabe su yi aiki tukuru wajen ganin samun nasarar jam’iyyar APC a kowani mataki a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCSiyasatakaraTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Mutuwar Abokai Biyu Ta Fallasa Lalacewar Asibitocin Jihar Neja

Next Post

Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

16 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

18 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

23 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

1 day ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

1 day ago
Next Post
Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.