• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Litar Mai Ka Iya Dawowa N900 A Bukukuwan Sabuwar Shekara – Dillalai

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Farashin Litar Mai Ka Iya Dawowa N900 A Bukukuwan Sabuwar Shekara – Dillalai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dillalan Man Fetur a Nijeriya sun ce da yiwuwar farashin litar man fetur ka iya rayuwa zuwa tsakanin naira 900 ko 1,000, lokutan bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara a bisa yunkurin matatar man Dangote.

Shugaban kungiyar masu sayar da mai a gidajen mai na kasa (PETROAN), Billy Gillis-Harry, da Kakakin kungiyar dillalan mai na kasa (IPMAN), Chinedu Ukadike, su ne suka shelanta hakan a ranar Litinin.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Gobara Ta Tashi A Gidan Rediyo A Legas

Wannan matakin na zuwa bayan da matatar man Dangote a ranar Lahadi ta rage farashin Litar mai da naira 20, inda ta dawo naira 970 daga naira 990 kan lita guda. Kamfanin ya yi bayanin cewa an yi hakan ne domin nuna godiya ga goyon bayan ‘yan Nijeriya.

Wannan kuma na zuwa ne bayan makonni da matatar ta sanya hannu da dillalai mai domin sayar musu da mai kai tsaye.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan, Gillis-Harry ya ce rigin farashin da matatar Dangote ta yi zai taimaki ‘yan Nijeriya sosai.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

A cewarsa, da yiwuwar farashin ma zai ci gaba da sauka amma ya danganta ne da farashin danyen mai da kuma matatar Dangote.

“Tabbas farashin zai ci gaba da raguwa nan gaba. Abu ne mai kyau ga masu jan ragamar da ‘yan Nijeriya,” ya shaida.

Kazalika, shi ma Ukadike ya tsugunta wa ‘yan Nijeriya cewa farashin mai da rahusa na nan tafe a wannan lokaci bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Ya bayyana cewa rage farashin man da matatar Dangote ta yi a baya-bayan nan ya nuna cewa farashin man fetur a duk gidajen mai na mambobin IPMAN zai ragu tsakanin naira 15 zuwa naira 20, ya dangane da wurin ko nisan gari.

Ukadike ya kara da cewa farashin man fetur mafi arha da ‘yan Nijeriya za su yi tsammani nan da Disamba 2024 ya kamata ya kasance tsakanin naira 900 zuwa naira 1000 kowace lita.

Idan dai za a iya tunawa a ranar Juma’ar makon da ya gabata ne Kamfanin Mai na Nijeriya ya shaida wa ‘yan kasuwar man da su dakatar da shigo da mai su maida hankali kan matatar ta Dangote.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DillalaiFarashiFetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Tashi A Gidan Rediyo A Legas

Next Post

Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

2 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

4 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

11 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

23 hours ago
Next Post
Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

LABARAI MASU NASABA

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.