ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Litar Mai Ka Iya Dawowa N900 A Bukukuwan Sabuwar Shekara – Dillalai

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Mai

Dillalan Man Fetur a Nijeriya sun ce da yiwuwar farashin litar man fetur ka iya rayuwa zuwa tsakanin naira 900 ko 1,000, lokutan bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara a bisa yunkurin matatar man Dangote.

Shugaban kungiyar masu sayar da mai a gidajen mai na kasa (PETROAN), Billy Gillis-Harry, da Kakakin kungiyar dillalan mai na kasa (IPMAN), Chinedu Ukadike, su ne suka shelanta hakan a ranar Litinin.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Gobara Ta Tashi A Gidan Rediyo A Legas

Wannan matakin na zuwa bayan da matatar man Dangote a ranar Lahadi ta rage farashin Litar mai da naira 20, inda ta dawo naira 970 daga naira 990 kan lita guda. Kamfanin ya yi bayanin cewa an yi hakan ne domin nuna godiya ga goyon bayan ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Wannan kuma na zuwa ne bayan makonni da matatar ta sanya hannu da dillalai mai domin sayar musu da mai kai tsaye.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan, Gillis-Harry ya ce rigin farashin da matatar Dangote ta yi zai taimaki ‘yan Nijeriya sosai.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A cewarsa, da yiwuwar farashin ma zai ci gaba da sauka amma ya danganta ne da farashin danyen mai da kuma matatar Dangote.

“Tabbas farashin zai ci gaba da raguwa nan gaba. Abu ne mai kyau ga masu jan ragamar da ‘yan Nijeriya,” ya shaida.

Kazalika, shi ma Ukadike ya tsugunta wa ‘yan Nijeriya cewa farashin mai da rahusa na nan tafe a wannan lokaci bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Ya bayyana cewa rage farashin man da matatar Dangote ta yi a baya-bayan nan ya nuna cewa farashin man fetur a duk gidajen mai na mambobin IPMAN zai ragu tsakanin naira 15 zuwa naira 20, ya dangane da wurin ko nisan gari.

Ukadike ya kara da cewa farashin man fetur mafi arha da ‘yan Nijeriya za su yi tsammani nan da Disamba 2024 ya kamata ya kasance tsakanin naira 900 zuwa naira 1000 kowace lita.

Idan dai za a iya tunawa a ranar Juma’ar makon da ya gabata ne Kamfanin Mai na Nijeriya ya shaida wa ‘yan kasuwar man da su dakatar da shigo da mai su maida hankali kan matatar ta Dangote.

Mai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

Gombe Da Gidauniyar ‘Bill & Melinda Gates’ Sun Hada Gwiwa Don Bunkasa Kiwon Lafiya Da Noma

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.