• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

by Abubakar Sulaiman
3 hours ago
Ritaya

Sauyin shugabannin rundunonin tsaro da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar a wannan mako zai haifar da murabus da ritayar fiye da janarori 50 daga rundunar Soji, bisa ga tsarin da ke tilasta manyan hafsoshi da suka fi sabon shugaban shekaru su ajiye aiki.

Bayan naɗin Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon Shugaban Rundunar Soji (Chief of Defence Staff), tare da sabbin shugabannin rundunonin ƙasa, da sama da manyan hafsoshi 50 da suka yi aiki tare da tsohon CDS, Janar Christopher Musa, za su tafi ritayar dole. Wannan ya haɗa da brigediyoyi, da janarori, da kwamandoji daga Sojojin ƙasa da na sama, da kuma na ruwa.

  • Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya
  • Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Masana harkokin tsaro sun bayyana cewa wannan tsarin “Ritayar Doke” yana da tarihi a cikin rundunar, amma sauyin da aka yi a wannan karon na iya shafar ƙwararrun hafsoshi da suka daɗe suna aiki. Wani tsohon kwamandan Soji, Janar Aliyu Gusau (mai ritaya), ya ce irin waɗannan sauye-sauye suna da amfani wajen sabunta rundunar, amma ya kamata gwamnati ta samar da tsarin tallafi ga waɗanda ake tura wa ritaya da wuri.

Wani binciken da jaridar Leadership Hausa ta gudanar ya nuna cewa mafi yawan waɗanda ke shirin ritaya sun fito ne daga rundunar sojin ƙasa, inda ake ganin sabbin naɗe-naɗen za su buƙaci sabon tsarin horo da maye gurbin manyan da zasu bar aiki.

Wasu ƙungiyoyin tsofaffin sojoji sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta sabunta tsarin fansho da walwalar masu ritaya, musamman ganin cewa akasarin waɗannan hafsoshi sun yi hidima tsawon shekaru 30 zuwa 35. Kungiyar Veterans for National Security ta ce “akwai buƙatar samar da tsarin taimakon gaggawa domin tabbatar da cewa waɗannan tsofaffin jarumai ba su fuskanci matsin tattalin arziƙi ba bayan ritaya ba shiri”

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

Sauyin shugabannin tsaro dai ya nuna matakin da Tinubu ke ɗauka wajen sake fasalin tsaro, amma kuma ya buɗe sabon babi na tattaunawa kan yadda ake kula da tsofaffin hafsoshin da suka ba ƙasa hidima tsawon shekaru.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce
Manyan Labarai

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin
Manyan Labarai

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.