• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gajartar Amarya Tasa Ango Ya Fasa Auren Amaryarsa Ana Tsaka Da Gudanar Da Biki

by Muhammad
3 years ago
in Al'ajabi
0
Gajartar Amarya Tasa Ango Ya Fasa Auren Amaryarsa Ana Tsaka Da Gudanar Da Biki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata budurwa ’yar kasar Tunisiya da take shirin zama amarya ta rika samun sakonnin tallafi daga sassan duniya bayan an yi watsi da bikin aurenta lokaci guda saboda sukar da surukarta ta yi mata cewa ba ta gamsu da yadda kamanninta yake ba.

Aminiya ta rawaito cewa, a karshen watan jiya ne wata budurwa mai suna Lamia al-Labawi, ta wallafa labari mai ban-tausayi a shafin Facebook inda ta bayyana yadda abin da ya kamata ya zama mafi alheri a rayuwarta ya koma wani mafarki mai ban tsoro.

  • Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Ma’aikata Hudu Da ‘Yansanda Biyu A Kamfanin Sarrafa Tasa

Ya kamata a ce an yi aurenta da angonta shekara hudu da suka wuce amma sai yanzu; an shirya komai kuma sun kashe makudan kudi don ganin komai ya tafi yadda aka tsara, amma abin da ba su yi la’akari da shi ba, shi ne furucin mahaifiyar ango.

Lamia ta ce, ba ta taba haduwa da mahaifiyar angonta ba, kuma maimakon a yi mata tarba cikin mutunci zuwa cikin danginsu, abin da ta samu a ranar aurenta shi ne munanan kalamai.

Bayan fara bikin daurin auren, baki sun hallara, surukar Lamia da wasu sun kudiri wani abu a zuciyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

A gaban kowa, surukar ta matso kusa da danta (angon) ta ba shi umarnin ya soke bikin auren, tana mai cewa amaryar “gajera ce kuma mummuna” da ba ta cancanci ta auri danta ba.

A baya hotunan Lamia ne kawai ta gani, kuma da alama ta ji takaici sosai bayan ganin amaryar ido da ido.

Cin mutuncin da uwar angon ta yi wa amaryar bai zama wani babban al’amari ba, sai dai bakin sun yi mamakin abin da angon ya yi.

Ya bi umarnin mahaifiyarsa, kuma duk rokon da mutane da yawa suka yi a wurin bikin, amma ya watsar da auran Lamia ya bar harabar bikin tare da mahaifiyarsa.

Nan da nan labarin ya bazu a shafukan sada zumunta, kuma Lamia al-Labawi ta fara samun sakonnin goyon baya daga mutanen da suke gaya mata cewa, ta dage ta kuma gane cewa angon bai cancanci yin aure ba.

“Tare da soyayya da ’yan uwantaka, ina gaya muku, ku daga kanku ku fuskanci duniya da dukkan karfinku,” Dan wasan kwaikwayo na Tunisiya, Hedi Al-Mejri, ya rubuta wa Lamia.

“Duniya tana dauke da darasi, kuma dole ne mutum ya bambance tsakanin miji da sauran maza. Ubangijina zai saka mata da alheri, insha Allahu za ta samu abu mai kyau a gaba.

“Auren Lamia darasi ne daga darussan rayuwa, kuma gaba ta fi kyau, insha Allahu,” wani mai suna Sana Cherif ya rubuta a Facebook.

Lamia al-Labawi ta fitar da wani faifan bidiyo tana gode wa kowa kan kalaman karfafa gwiwa da suka aike mata. Abin da za a iya cewa game da angon shi ne, akalla bai yi watsi da auren a kashin kansa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Next Post

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

2 months ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

2 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

3 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

4 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

4 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

4 months ago
Next Post
An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.