• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gajartar Amarya Tasa Ango Ya Fasa Auren Amaryarsa Ana Tsaka Da Gudanar Da Biki

by Muhammad
3 years ago
in Al'ajabi
0
Gajartar Amarya Tasa Ango Ya Fasa Auren Amaryarsa Ana Tsaka Da Gudanar Da Biki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata budurwa ’yar kasar Tunisiya da take shirin zama amarya ta rika samun sakonnin tallafi daga sassan duniya bayan an yi watsi da bikin aurenta lokaci guda saboda sukar da surukarta ta yi mata cewa ba ta gamsu da yadda kamanninta yake ba.

Aminiya ta rawaito cewa, a karshen watan jiya ne wata budurwa mai suna Lamia al-Labawi, ta wallafa labari mai ban-tausayi a shafin Facebook inda ta bayyana yadda abin da ya kamata ya zama mafi alheri a rayuwarta ya koma wani mafarki mai ban tsoro.

  • Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Ma’aikata Hudu Da ‘Yansanda Biyu A Kamfanin Sarrafa Tasa

Ya kamata a ce an yi aurenta da angonta shekara hudu da suka wuce amma sai yanzu; an shirya komai kuma sun kashe makudan kudi don ganin komai ya tafi yadda aka tsara, amma abin da ba su yi la’akari da shi ba, shi ne furucin mahaifiyar ango.

Lamia ta ce, ba ta taba haduwa da mahaifiyar angonta ba, kuma maimakon a yi mata tarba cikin mutunci zuwa cikin danginsu, abin da ta samu a ranar aurenta shi ne munanan kalamai.

Bayan fara bikin daurin auren, baki sun hallara, surukar Lamia da wasu sun kudiri wani abu a zuciyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

A gaban kowa, surukar ta matso kusa da danta (angon) ta ba shi umarnin ya soke bikin auren, tana mai cewa amaryar “gajera ce kuma mummuna” da ba ta cancanci ta auri danta ba.

A baya hotunan Lamia ne kawai ta gani, kuma da alama ta ji takaici sosai bayan ganin amaryar ido da ido.

Cin mutuncin da uwar angon ta yi wa amaryar bai zama wani babban al’amari ba, sai dai bakin sun yi mamakin abin da angon ya yi.

Ya bi umarnin mahaifiyarsa, kuma duk rokon da mutane da yawa suka yi a wurin bikin, amma ya watsar da auran Lamia ya bar harabar bikin tare da mahaifiyarsa.

Nan da nan labarin ya bazu a shafukan sada zumunta, kuma Lamia al-Labawi ta fara samun sakonnin goyon baya daga mutanen da suke gaya mata cewa, ta dage ta kuma gane cewa angon bai cancanci yin aure ba.

“Tare da soyayya da ’yan uwantaka, ina gaya muku, ku daga kanku ku fuskanci duniya da dukkan karfinku,” Dan wasan kwaikwayo na Tunisiya, Hedi Al-Mejri, ya rubuta wa Lamia.

“Duniya tana dauke da darasi, kuma dole ne mutum ya bambance tsakanin miji da sauran maza. Ubangijina zai saka mata da alheri, insha Allahu za ta samu abu mai kyau a gaba.

“Auren Lamia darasi ne daga darussan rayuwa, kuma gaba ta fi kyau, insha Allahu,” wani mai suna Sana Cherif ya rubuta a Facebook.

Lamia al-Labawi ta fitar da wani faifan bidiyo tana gode wa kowa kan kalaman karfafa gwiwa da suka aike mata. Abin da za a iya cewa game da angon shi ne, akalla bai yi watsi da auren a kashin kansa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Next Post

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

Related

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

3 weeks ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 month ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 month ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

3 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

4 months ago
Next Post
An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027

Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

June 15, 2025
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

June 15, 2025
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

June 15, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

June 15, 2025
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

June 15, 2025
UEFA

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

June 15, 2025
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.