• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Kungiyoyin Kasuwar Sabon Gari Sun Jajanta Wa ‘Yan Kasuwan Kwari Da Na Titin Bairut

by Ibrahim Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Gamayyar Kungiyoyin Kasuwar Sabon Gari Sun Jajanta Wa ‘Yan Kasuwan Kwari Da Na Titin Bairut
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayya kungiyar ‘yan kasuwar Muhammad Abubakar Rimi da akafi kira da Kasuwar Sabon Gari karkashin shugabancin Alhaji Aminu Mu’awiyya Dala sun jajanta wa ‘yan uwansu ‘yan kasuwar kantin Kwari da na kan titin Bairut bisa iftila’in ambaliyar ruwa da rugujewar gini daya jawo samun raunuka da asarar dukiya. 

Da yake magana a madadin shugaban kungiyar, jami’in hulda da jama’a na kungiyar Salihu Ibrahim Darma ya ce wannan abu ya damesu a matsayinsu na ‘yan kasuwa wannan abu ya faru ne a sanadiyyar gine-gine da aka yi barkatai ba a bisa ka’ida ba, ana toshe hanyoyi magudanan ruwa.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Gwamna Buni Ya Cika Alkawarin Saya Wa Iyalan Sheikh Goni Aisami Gidaje

Ya kara da cewa duk da sun gamsu da matakinda Gwamnan Kano ya dauka na ba da umurnin gaggawa na rushe duk wani gini da ake ganin shi ya jawo ambaliyar ruwar da aka yi a Kantin kwari sai dai suna kira ga Gwamnati ta sanya yan kasuwa a cikin kwamitinda ta kafa da za su yi aikin rushe gineginen domin su suka san duk wasu gine-gine da akayi da sune musabbabin jawo ambaliyar da Gwamnan bai san dasu ba, muddin ba su aka kawar ba, za a cigaba da samun cigaba da ambaliyar.

Darma ya ce ba kasuwar ta Kantin Kwari kadai ba yawanci kasuwanni da suke Jihar Kano akwai irin wadannan matsaloli na yin gini ba bisa ka’ida ba kuma hakan na faruwa ne da sahalewar hukumomi, hakan tasa yan kasuwar sun yita korafe-korafe da kokawa ga Gwamnati a kan lamarin takai har wasu sun je kotu, amma abin takaici ko bayan da kotu ta bada umurnin a dakatar da gine-ginen sai ayi biris da umurnin a cigaba.

Ya yi nuni da cewa ko a kasuwarsu ta Sabon gari akwai ginegine na toshe hanyoyi da kofofin da hukumar Kasuwar tayi kuma sun kai kuka ga hukumomi har majalisar jiha, amma ba wani mataki da aka dauka akai daga bisani suka je kotu amma ba abinda ya sauya.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Ya yi nuni da cewa irin wannan abin Allah ya kiyaye in wani hatsari ta faru kamar na gobara babu ta inda za a iya kai dauki na gaggawa saboda duk an yi gine-gine da suka toshe hanyoyi.

Darma ya ce yakamata hukumomi su rika daukar mataki akan duk wani jami’in hukuma da ya yi abinda ya sabawa doka da ka iya cutar da al’umma. Tare da yin fatan Allah ya mayar da alkhairi ga yan kasuwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BerutJajeKasuwaSabon Gari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

Next Post

Zan Yi Iyakar Kokarina Wajen Bunkasa Karamar Hukuma Garko A Jihar Kano -Salisu Musa Sarina

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

36 minutes ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

2 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

3 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

4 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

6 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

6 hours ago
Next Post
Zan Yi Iyakar Kokarina Wajen Bunkasa Karamar Hukuma Garko A Jihar Kano -Salisu Musa Sarina

Zan Yi Iyakar Kokarina Wajen Bunkasa Karamar Hukuma Garko A Jihar Kano -Salisu Musa Sarina

LABARAI MASU NASABA

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.