ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Kungiyoyin Kasuwar Sabon Gari Sun Jajanta Wa ‘Yan Kasuwan Kwari Da Na Titin Bairut

by Ibrahim Muhammad
4 years ago
Sabon Gari

Gamayya kungiyar ‘yan kasuwar Muhammad Abubakar Rimi da akafi kira da Kasuwar Sabon Gari karkashin shugabancin Alhaji Aminu Mu’awiyya Dala sun jajanta wa ‘yan uwansu ‘yan kasuwar kantin Kwari da na kan titin Bairut bisa iftila’in ambaliyar ruwa da rugujewar gini daya jawo samun raunuka da asarar dukiya. 

Da yake magana a madadin shugaban kungiyar, jami’in hulda da jama’a na kungiyar Salihu Ibrahim Darma ya ce wannan abu ya damesu a matsayinsu na ‘yan kasuwa wannan abu ya faru ne a sanadiyyar gine-gine da aka yi barkatai ba a bisa ka’ida ba, ana toshe hanyoyi magudanan ruwa.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Gwamna Buni Ya Cika Alkawarin Saya Wa Iyalan Sheikh Goni Aisami Gidaje

Ya kara da cewa duk da sun gamsu da matakinda Gwamnan Kano ya dauka na ba da umurnin gaggawa na rushe duk wani gini da ake ganin shi ya jawo ambaliyar ruwar da aka yi a Kantin kwari sai dai suna kira ga Gwamnati ta sanya yan kasuwa a cikin kwamitinda ta kafa da za su yi aikin rushe gineginen domin su suka san duk wasu gine-gine da akayi da sune musabbabin jawo ambaliyar da Gwamnan bai san dasu ba, muddin ba su aka kawar ba, za a cigaba da samun cigaba da ambaliyar.

ADVERTISEMENT

Darma ya ce ba kasuwar ta Kantin Kwari kadai ba yawanci kasuwanni da suke Jihar Kano akwai irin wadannan matsaloli na yin gini ba bisa ka’ida ba kuma hakan na faruwa ne da sahalewar hukumomi, hakan tasa yan kasuwar sun yita korafe-korafe da kokawa ga Gwamnati a kan lamarin takai har wasu sun je kotu, amma abin takaici ko bayan da kotu ta bada umurnin a dakatar da gine-ginen sai ayi biris da umurnin a cigaba.

Ya yi nuni da cewa ko a kasuwarsu ta Sabon gari akwai ginegine na toshe hanyoyi da kofofin da hukumar Kasuwar tayi kuma sun kai kuka ga hukumomi har majalisar jiha, amma ba wani mataki da aka dauka akai daga bisani suka je kotu amma ba abinda ya sauya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Ya yi nuni da cewa irin wannan abin Allah ya kiyaye in wani hatsari ta faru kamar na gobara babu ta inda za a iya kai dauki na gaggawa saboda duk an yi gine-gine da suka toshe hanyoyi.

Darma ya ce yakamata hukumomi su rika daukar mataki akan duk wani jami’in hukuma da ya yi abinda ya sabawa doka da ka iya cutar da al’umma. Tare da yin fatan Allah ya mayar da alkhairi ga yan kasuwar.

Sabon Gari
Ibrahim Muhammad
+ postsBio
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Za Mu Yi Gwagwarmayar Ƙwato Haƙƙin Ƴan Takarar Da Aka Zalunta A Jam’iyyar ADC —Mainasara Salga
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Ba Mu San Da Ficewar Hanga Da Gaya Daga Jam’iyyar NDC Ba A Hukumance —Hussaini Isah Meriga
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
  • Ibrahim Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-muhammad/
    Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Zan Yi Iyakar Kokarina Wajen Bunkasa Karamar Hukuma Garko A Jihar Kano -Salisu Musa Sarina

Zan Yi Iyakar Kokarina Wajen Bunkasa Karamar Hukuma Garko A Jihar Kano -Salisu Musa Sarina

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.