• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Kungiyoyin Sun Bukaci Buhari Da APC Su Zabi Boss Mustapha A Mataimakin Tinubu

by Muhammad
3 years ago
Gamayyar

Gamayyar kungiyoyin rajin kare hakkin dimokradiyya da fararen hula, sun roki shugaban kasa, Muhammadu Buhari da jam’iyyar APC da su amince da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bai wa jam’iyyun siyasa wa’adin zuwa ranar Juma’a 17 ga watan Yunin 2022 da su mika sunayen ‘yan takararsu na shugaban kasa da mataimakinsa ga hukumar.

  • 2023: Wasu ‘Yan Jam’iyyar APC Sun Nemi Tinubu Ya Dauki Gwamnan Neja Mataimaki
  • 2023: Ban Ce Zan Dauki Mataimaki Musulmi Ba – Tinubu

A wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba, gamayyar kungiyoyin da suka hada da kungiyar kare hakkin ‘yan asalin kasa (PAIR) da Civil Society Action for National Inclusion (CSANI), da Society for Equity and Gender Advocacy (SEGA), sun ce, Mustapha ya yi fice a cikin duk wasu da ake yi wa hasashen basu mataimakin.

“Boss Mustapha mai rikon amana ne kuma ba shi da wata hayaniya ko wani cikas da zai durkusar da shirin APC na ci gaba da rike madafun iko a 2023,”

“A matsayinsa na Kiristan Arewa, mustapha zai dace da ma’aunin da ake bukata, tare da rage fargaba a wurin al’umar Kirista. da kuma tabbatar da cewa za a kare muradun Arewa,” in ji kungiyar.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

A cikin sanarwar da Isa Pai, Chukwudi Emmanuel da Fola Akin suka sanya wa hannu, sun bayyana cewa, “a tsawon shekaru, Boss Mustapha, sakataren gwamnatin tarayya ya nuna kwazo a cikin ayyukansa, jajircewa da kuma biyayya ga manufofin shugaban kasa Muhammadu. Buhari.

“A matsayinsa na shugaban kwamitin shugaban kasa kan COVID-19, Boss Mustapha ya nuna cewa yana iya aiwatar da lamuran da Suka shafi kasa cikin gaggawa, abin da ake bukata shi ne mutumin da zai iya jagoranci, tsarawa, kai tsaye da mayar da hankali.”

Don haka kungiyar ta yi kira ga “Shugaba Muhammadu Buhari da shugabannin jam’iyyar APC da su aiwatar kamar yadda suka saba yi.

“Yayin da gaba ta karshe ko gab da kammala zaben dan takarar mataimakin shugaban kasa, Boss Mustapha ya fi kowa dacewa a halin yanzu ta fuskar tarihinsa mara lahani, aikin gwamnati da kasa, alkibla da manufa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.