• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Kungiyoyin Sun Bukaci Buhari Da APC Su Zabi Boss Mustapha A Mataimakin Tinubu

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
Gamayyar Kungiyoyin Sun Bukaci Buhari Da APC Su Zabi Boss Mustapha A Mataimakin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar kungiyoyin rajin kare hakkin dimokradiyya da fararen hula, sun roki shugaban kasa, Muhammadu Buhari da jam’iyyar APC da su amince da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bai wa jam’iyyun siyasa wa’adin zuwa ranar Juma’a 17 ga watan Yunin 2022 da su mika sunayen ‘yan takararsu na shugaban kasa da mataimakinsa ga hukumar.

  • 2023: Wasu ‘Yan Jam’iyyar APC Sun Nemi Tinubu Ya Dauki Gwamnan Neja Mataimaki
  • 2023: Ban Ce Zan Dauki Mataimaki Musulmi Ba – Tinubu

A wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba, gamayyar kungiyoyin da suka hada da kungiyar kare hakkin ‘yan asalin kasa (PAIR) da Civil Society Action for National Inclusion (CSANI), da Society for Equity and Gender Advocacy (SEGA), sun ce, Mustapha ya yi fice a cikin duk wasu da ake yi wa hasashen basu mataimakin.

“Boss Mustapha mai rikon amana ne kuma ba shi da wata hayaniya ko wani cikas da zai durkusar da shirin APC na ci gaba da rike madafun iko a 2023,”

“A matsayinsa na Kiristan Arewa, mustapha zai dace da ma’aunin da ake bukata, tare da rage fargaba a wurin al’umar Kirista. da kuma tabbatar da cewa za a kare muradun Arewa,” in ji kungiyar.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

A cikin sanarwar da Isa Pai, Chukwudi Emmanuel da Fola Akin suka sanya wa hannu, sun bayyana cewa, “a tsawon shekaru, Boss Mustapha, sakataren gwamnatin tarayya ya nuna kwazo a cikin ayyukansa, jajircewa da kuma biyayya ga manufofin shugaban kasa Muhammadu. Buhari.

“A matsayinsa na shugaban kwamitin shugaban kasa kan COVID-19, Boss Mustapha ya nuna cewa yana iya aiwatar da lamuran da Suka shafi kasa cikin gaggawa, abin da ake bukata shi ne mutumin da zai iya jagoranci, tsarawa, kai tsaye da mayar da hankali.”

Don haka kungiyar ta yi kira ga “Shugaba Muhammadu Buhari da shugabannin jam’iyyar APC da su aiwatar kamar yadda suka saba yi.

“Yayin da gaba ta karshe ko gab da kammala zaben dan takarar mataimakin shugaban kasa, Boss Mustapha ya fi kowa dacewa a halin yanzu ta fuskar tarihinsa mara lahani, aikin gwamnati da kasa, alkibla da manufa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBoss MustaphaBuhariKungiyoyiMataimakin Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

Next Post

‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

1 day ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 day ago
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
Siyasa

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

2 days ago
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu
Siyasa

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

2 days ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.