• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Siyasar Kwankwaso Da el-Rufai A Sikeli

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya kai wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufa’I ziyara a gidansa da ke Abuja, jama’a suke ta fadin albarkacin bakinsu kan wannan ganawar na jiga-jigan ‘yan siyasa, wanda sanin kowa ne ganawar tana da alaka da tunkarar zaben 2027, domin kuwa su kansu ‘yan siyasa sun sana cewa, ‘sai an hada karfi da karfe sannan za a kai ga gaci.

Kwankwaso da el-Rufai suna da kamanceceniya a wasu abubuwa guda 10 da suka hada da:
Dukkanninsu dai sun yi gwamna na shekara takwas-takwas a jihohinsu kuma sun rike mukamin minista na zango, inda Kwankwaso ya yi ministan tsaro, yayin da el-Rufai ya yi ministan Babban Birnin Tarayya Abuja.
Haka kuma dukkaninsu sun nada magadansu a lokacin da za su bar mukamin gwamna a jihohinsu, kuma daga baya wadannan magadan nasu suka butulce masu suka koma abokannin adawarsu.

  • Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku
  • Rahoto Ya Bankado ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaron Nijeriya 200 Masu Kadarori A Dubai

Kazalika, dukkanin suna amfani da ikon da suke da shi wajen danne kowa, hakan ya sanya ake yi wa kowa lakabi da karfin ikon da yake da shi. Inda ake yi wa Kwankwaso lakabi da ‘DanMusa mai takalmin karfe, kowa ka taka ya taku,’ shi kuma el-Rufai ake yi masa lakabi da ‘Mai Rusau’.

Sannan kuma dukkansu an zarge su da badakkala da kudaden gwamnati a lokacin da suke madafun iko, inda aka rika sa-toka, sa-katsi tsakaninsu da hukumomin yaki da rashawa.

Dukkansu sun taka muhimmiyar rawa wajen bai wa jam’iyyar gwamnati damar yin nasara a zaben 2023, inda Kwankwaso ya fito takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, yayin da el-Rufai kuma ya yi ruwa ya yi tsaki wajen tallata kudirin takarar musulmi da musulmi a yankin arewa har aka kai gaci, wato jam’iyyar APC ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Kwankwaso da el-Rufai sun nuna ra’ayinsu na zama shugaban kasa wanda suka nuna kwadayinsu a kan yankin arewa, domin idan sun sami nasara a arewa sun rage aiki.
Dukkaninsu kyankyasar jam’iyyar PDP ne wadanda suka bar jam’iyyar, a yanzu kuma suke son angulu ta koma gidanta na tsamiya.

Haka kuma dukkaninsu sun so su yi aiki a cikin gwamnatin Tinubu, amma ba su sami dama ba.
Kwankwaso da el-Rufai dukkansu dai barazanar siyasa ne ga Shugaban kasa Bola Tinubu, inda za su iya kasancewa masu adawa mai karfi da zai kawo karshen tuninsa na zarcewa a kan karagar mulki karo na biyu da Tinubu ke muradi.

Lallai wadannan jiga-jigan siyasar suna bukatar junansu duk da irin bambance-bambancen da ke tsakaninsu wajen cimma muradinsu a siyasance. Don ko a falsafar siyasa ana cewa ‘abokin adawa, abokin hamayyata, abokina ne’.

A bangare guda kuma, shugaban kungiyar ci gaba matasa (AYCF), Yerima Shettima ya bayyana cewa ganawar Kwankwaso da el-Rufai makarkashiya ce ga mulkin Tinubu.

Shettima ya nuna fargabarsa kan ganawar Kwankwaso da el-Rufai ne a lokacin da yake zantawa da Jaridar LEADERSHIP a karshen mako.

Da yake tabbatar da ganawar, Kwankwaso a cikin sakonsa na kafar sada zumunta ta Tuwita ya ce, “Ina son in kai ziyarar gaisuwa ga tsohon abokin aikina, H.E Nasir el-Rufai, a gidansa da ke Abuja a yau.”
Har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan tattaunawar tasu ba, amma wata majiya da ke kusa da su ta yi nuni da cewa, ganawar ta kasance wani bangare ne na gina tsohuwar alaka da kawance da ka iya kaiwa ga kawancen siyasa gabanin babban zaben 2027.

Sai dai wani jigo a jam’iyyar APC, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ganawar ba wani abu ba ne illa taron mutanen da aka fusata, na neman su dawo da martabarsu.

Wannan ita ce ganawa ta farko a tsakanin el-Rufai wanda ya kasance nag aba-gaba wajen yakin neman zaben Tinubu a 2023 da Kwankwaso wanda ya zo na hudu a zaben tun bayan a aka kammala zaben shugaban kasan.

Duk da cewa el-Rufai ya ci gaba da zama jigo a jam’iyyar APC, tun bayan da ya rasa samun mukamin minista bayan majalisar dattawa ta ki amincewa da nadin nasa.

Yanzu haka dai el-Rufai da Kwankwaso na ci gaba da fuskantar rikicin siyasa a jihohinsu.
Kwankwaso na fuskantar rikicin da ya barke kan kujerar Sarkin Kano da kuma tuhumar da ake yi wa tsohon gwamnan jihar, Dakta Abdullahi Ganduje, ya kara dagula lissafi, tsakanin Kwankwaso jagoran jam’iyyar NNPP ta Kano da Ganduje shugaban APC na kasa.

A Kaduna kuwa, rashin jituwar da ke tsakanin el-Rufai da Gwamna Uba Sani, wanda ya gada shi kuma yaronsa a siyasa, ya kai ga tuhumi tsohon gwamnan da majalisar dokokin Jihar Kaduna ta yi a kan zargin karkatar da naira biliyan 432, zargin da el-Rufai ya kalubalanta a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaKwankwasoSiyasar Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi: Ziyarar Xi Ya Zurfafa Dangantakar Kasashe Makwabta

Next Post

Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

12 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kwankwaso

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.