• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Siyasar Kwankwaso Da el-Rufai A Sikeli

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya kai wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufa’I ziyara a gidansa da ke Abuja, jama’a suke ta fadin albarkacin bakinsu kan wannan ganawar na jiga-jigan ‘yan siyasa, wanda sanin kowa ne ganawar tana da alaka da tunkarar zaben 2027, domin kuwa su kansu ‘yan siyasa sun sana cewa, ‘sai an hada karfi da karfe sannan za a kai ga gaci.

Kwankwaso da el-Rufai suna da kamanceceniya a wasu abubuwa guda 10 da suka hada da:
Dukkanninsu dai sun yi gwamna na shekara takwas-takwas a jihohinsu kuma sun rike mukamin minista na zango, inda Kwankwaso ya yi ministan tsaro, yayin da el-Rufai ya yi ministan Babban Birnin Tarayya Abuja.
Haka kuma dukkaninsu sun nada magadansu a lokacin da za su bar mukamin gwamna a jihohinsu, kuma daga baya wadannan magadan nasu suka butulce masu suka koma abokannin adawarsu.

  • Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku
  • Rahoto Ya Bankado ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaron Nijeriya 200 Masu Kadarori A Dubai

Kazalika, dukkanin suna amfani da ikon da suke da shi wajen danne kowa, hakan ya sanya ake yi wa kowa lakabi da karfin ikon da yake da shi. Inda ake yi wa Kwankwaso lakabi da ‘DanMusa mai takalmin karfe, kowa ka taka ya taku,’ shi kuma el-Rufai ake yi masa lakabi da ‘Mai Rusau’.

Sannan kuma dukkansu an zarge su da badakkala da kudaden gwamnati a lokacin da suke madafun iko, inda aka rika sa-toka, sa-katsi tsakaninsu da hukumomin yaki da rashawa.

Dukkansu sun taka muhimmiyar rawa wajen bai wa jam’iyyar gwamnati damar yin nasara a zaben 2023, inda Kwankwaso ya fito takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, yayin da el-Rufai kuma ya yi ruwa ya yi tsaki wajen tallata kudirin takarar musulmi da musulmi a yankin arewa har aka kai gaci, wato jam’iyyar APC ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Kwankwaso da el-Rufai sun nuna ra’ayinsu na zama shugaban kasa wanda suka nuna kwadayinsu a kan yankin arewa, domin idan sun sami nasara a arewa sun rage aiki.
Dukkaninsu kyankyasar jam’iyyar PDP ne wadanda suka bar jam’iyyar, a yanzu kuma suke son angulu ta koma gidanta na tsamiya.

Haka kuma dukkaninsu sun so su yi aiki a cikin gwamnatin Tinubu, amma ba su sami dama ba.
Kwankwaso da el-Rufai dukkansu dai barazanar siyasa ne ga Shugaban kasa Bola Tinubu, inda za su iya kasancewa masu adawa mai karfi da zai kawo karshen tuninsa na zarcewa a kan karagar mulki karo na biyu da Tinubu ke muradi.

Lallai wadannan jiga-jigan siyasar suna bukatar junansu duk da irin bambance-bambancen da ke tsakaninsu wajen cimma muradinsu a siyasance. Don ko a falsafar siyasa ana cewa ‘abokin adawa, abokin hamayyata, abokina ne’.

A bangare guda kuma, shugaban kungiyar ci gaba matasa (AYCF), Yerima Shettima ya bayyana cewa ganawar Kwankwaso da el-Rufai makarkashiya ce ga mulkin Tinubu.

Shettima ya nuna fargabarsa kan ganawar Kwankwaso da el-Rufai ne a lokacin da yake zantawa da Jaridar LEADERSHIP a karshen mako.

Da yake tabbatar da ganawar, Kwankwaso a cikin sakonsa na kafar sada zumunta ta Tuwita ya ce, “Ina son in kai ziyarar gaisuwa ga tsohon abokin aikina, H.E Nasir el-Rufai, a gidansa da ke Abuja a yau.”
Har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan tattaunawar tasu ba, amma wata majiya da ke kusa da su ta yi nuni da cewa, ganawar ta kasance wani bangare ne na gina tsohuwar alaka da kawance da ka iya kaiwa ga kawancen siyasa gabanin babban zaben 2027.

Sai dai wani jigo a jam’iyyar APC, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ganawar ba wani abu ba ne illa taron mutanen da aka fusata, na neman su dawo da martabarsu.

Wannan ita ce ganawa ta farko a tsakanin el-Rufai wanda ya kasance nag aba-gaba wajen yakin neman zaben Tinubu a 2023 da Kwankwaso wanda ya zo na hudu a zaben tun bayan a aka kammala zaben shugaban kasan.

Duk da cewa el-Rufai ya ci gaba da zama jigo a jam’iyyar APC, tun bayan da ya rasa samun mukamin minista bayan majalisar dattawa ta ki amincewa da nadin nasa.

Yanzu haka dai el-Rufai da Kwankwaso na ci gaba da fuskantar rikicin siyasa a jihohinsu.
Kwankwaso na fuskantar rikicin da ya barke kan kujerar Sarkin Kano da kuma tuhumar da ake yi wa tsohon gwamnan jihar, Dakta Abdullahi Ganduje, ya kara dagula lissafi, tsakanin Kwankwaso jagoran jam’iyyar NNPP ta Kano da Ganduje shugaban APC na kasa.

A Kaduna kuwa, rashin jituwar da ke tsakanin el-Rufai da Gwamna Uba Sani, wanda ya gada shi kuma yaronsa a siyasa, ya kai ga tuhumi tsohon gwamnan da majalisar dokokin Jihar Kaduna ta yi a kan zargin karkatar da naira biliyan 432, zargin da el-Rufai ya kalubalanta a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaKwankwasoSiyasar Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi: Ziyarar Xi Ya Zurfafa Dangantakar Kasashe Makwabta

Next Post

Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 hour ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

11 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

12 hours ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.