ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Siyasar Kwankwaso Da el-Rufai A Sikeli

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
kwankwaso

Tun bayan da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya kai wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru el-Rufa’I ziyara a gidansa da ke Abuja, jama’a suke ta fadin albarkacin bakinsu kan wannan ganawar na jiga-jigan ‘yan siyasa, wanda sanin kowa ne ganawar tana da alaka da tunkarar zaben 2027, domin kuwa su kansu ‘yan siyasa sun sana cewa, ‘sai an hada karfi da karfe sannan za a kai ga gaci.

Kwankwaso da el-Rufai suna da kamanceceniya a wasu abubuwa guda 10 da suka hada da:
Dukkanninsu dai sun yi gwamna na shekara takwas-takwas a jihohinsu kuma sun rike mukamin minista na zango, inda Kwankwaso ya yi ministan tsaro, yayin da el-Rufai ya yi ministan Babban Birnin Tarayya Abuja.
Haka kuma dukkaninsu sun nada magadansu a lokacin da za su bar mukamin gwamna a jihohinsu, kuma daga baya wadannan magadan nasu suka butulce masu suka koma abokannin adawarsu.

  • Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku
  • Rahoto Ya Bankado ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaron Nijeriya 200 Masu Kadarori A Dubai

Kazalika, dukkanin suna amfani da ikon da suke da shi wajen danne kowa, hakan ya sanya ake yi wa kowa lakabi da karfin ikon da yake da shi. Inda ake yi wa Kwankwaso lakabi da ‘DanMusa mai takalmin karfe, kowa ka taka ya taku,’ shi kuma el-Rufai ake yi masa lakabi da ‘Mai Rusau’.

ADVERTISEMENT

Sannan kuma dukkansu an zarge su da badakkala da kudaden gwamnati a lokacin da suke madafun iko, inda aka rika sa-toka, sa-katsi tsakaninsu da hukumomin yaki da rashawa.

Dukkansu sun taka muhimmiyar rawa wajen bai wa jam’iyyar gwamnati damar yin nasara a zaben 2023, inda Kwankwaso ya fito takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, yayin da el-Rufai kuma ya yi ruwa ya yi tsaki wajen tallata kudirin takarar musulmi da musulmi a yankin arewa har aka kai gaci, wato jam’iyyar APC ta lashe zaben shugaban kasa a 2023.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Kwankwaso da el-Rufai sun nuna ra’ayinsu na zama shugaban kasa wanda suka nuna kwadayinsu a kan yankin arewa, domin idan sun sami nasara a arewa sun rage aiki.
Dukkaninsu kyankyasar jam’iyyar PDP ne wadanda suka bar jam’iyyar, a yanzu kuma suke son angulu ta koma gidanta na tsamiya.

Haka kuma dukkaninsu sun so su yi aiki a cikin gwamnatin Tinubu, amma ba su sami dama ba.
Kwankwaso da el-Rufai dukkansu dai barazanar siyasa ne ga Shugaban kasa Bola Tinubu, inda za su iya kasancewa masu adawa mai karfi da zai kawo karshen tuninsa na zarcewa a kan karagar mulki karo na biyu da Tinubu ke muradi.

Lallai wadannan jiga-jigan siyasar suna bukatar junansu duk da irin bambance-bambancen da ke tsakaninsu wajen cimma muradinsu a siyasance. Don ko a falsafar siyasa ana cewa ‘abokin adawa, abokin hamayyata, abokina ne’.

A bangare guda kuma, shugaban kungiyar ci gaba matasa (AYCF), Yerima Shettima ya bayyana cewa ganawar Kwankwaso da el-Rufai makarkashiya ce ga mulkin Tinubu.

Shettima ya nuna fargabarsa kan ganawar Kwankwaso da el-Rufai ne a lokacin da yake zantawa da Jaridar LEADERSHIP a karshen mako.

Da yake tabbatar da ganawar, Kwankwaso a cikin sakonsa na kafar sada zumunta ta Tuwita ya ce, “Ina son in kai ziyarar gaisuwa ga tsohon abokin aikina, H.E Nasir el-Rufai, a gidansa da ke Abuja a yau.”
Har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan tattaunawar tasu ba, amma wata majiya da ke kusa da su ta yi nuni da cewa, ganawar ta kasance wani bangare ne na gina tsohuwar alaka da kawance da ka iya kaiwa ga kawancen siyasa gabanin babban zaben 2027.

Sai dai wani jigo a jam’iyyar APC, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ganawar ba wani abu ba ne illa taron mutanen da aka fusata, na neman su dawo da martabarsu.

Wannan ita ce ganawa ta farko a tsakanin el-Rufai wanda ya kasance nag aba-gaba wajen yakin neman zaben Tinubu a 2023 da Kwankwaso wanda ya zo na hudu a zaben tun bayan a aka kammala zaben shugaban kasan.

Duk da cewa el-Rufai ya ci gaba da zama jigo a jam’iyyar APC, tun bayan da ya rasa samun mukamin minista bayan majalisar dattawa ta ki amincewa da nadin nasa.

Yanzu haka dai el-Rufai da Kwankwaso na ci gaba da fuskantar rikicin siyasa a jihohinsu.
Kwankwaso na fuskantar rikicin da ya barke kan kujerar Sarkin Kano da kuma tuhumar da ake yi wa tsohon gwamnan jihar, Dakta Abdullahi Ganduje, ya kara dagula lissafi, tsakanin Kwankwaso jagoran jam’iyyar NNPP ta Kano da Ganduje shugaban APC na kasa.

A Kaduna kuwa, rashin jituwar da ke tsakanin el-Rufai da Gwamna Uba Sani, wanda ya gada shi kuma yaronsa a siyasa, ya kai ga tuhumi tsohon gwamnan da majalisar dokokin Jihar Kaduna ta yi a kan zargin karkatar da naira biliyan 432, zargin da el-Rufai ya kalubalanta a gaban kotu.

Kwankwaso
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

Mun Nemi A Yi Binciken Gwamnatin El-Rufa’i A Bainar Jama’a, Majalisar Kaduna Ta Ki – Tsohon Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.