ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Maka Buhari A Kotun Koli Kan Batu Canjin Kudi 

by Sadiq
3 years ago
Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje

Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano ya maka Shugaba Muhammadu Buhari kara a gaban Kotun Koli kan sauya fasalin da aka yi wa takardun naira.

A watan Oktoban bara ne dai Babban Bankin Najeriya CBN bisa amincewar Shugaba Buhari ya sauya fasalin wasu daga cikin manyan kudin kasar na naira 200 da 500 da 1,000.

  • APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
  • Bayan Shafe Shekaru 32 Yana Limanci A Harami Sheikh Shuraim, Ya Nemi Uzurin Ajiye Limancin

A karar mai lamba SC/CS/200/2023 wadda Babban Lauyan Jihar Kano ya shigar ta hannun Sunusi Musa, Babban Lauya a Najeriya (SAN), Gwamnatin Kano ta ayyana cewa Shugaba Buhari shi kadai ba shi da hurumin umartar CBN dakatar da tsoffin takardun kudin da aka sauyawa fasali.

ADVERTISEMENT

Aminiya ta ruwaito cewa, karar wadda Gwamnatin Kano ta gabatar a jiya Alhamis, ta kafa hujjar cewa Buhari ba shi da wannan hurumi ba tare da tuntuba da amincewar Majalisar Tattalin Arziki da kuma Majalisar Zartarwa ta kasar ba.

A bisa wannan madogara ce Gwamnatin Kano ta bukaci Kotun Kolin ta soke matakin Babban Bankin na janye takardun kudaden saboda abin ta kira wahalar da al’ummar jihar ke ciki.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

A tattaunawarsa da manema labarai, Babban Lauyan da ya shigar da karar Sunusi Musa ya ce a ranar Laraba ne kotun za ta saurari karar.

Kazalika, Gwamnatin Kanon tana son kotun ta bayar da umarnin da zai tilasta wa Gwamnatin Tarayya ta soke shirin nata na sauyin kudi saboda a cewarta ya saba wa Kundin Tsarin Mulkin Kasar na 1999.

An kuma ruwaito cewa Gwamnatin Kanon tana bukatar Kotun Kolin ta zartar cewa umarnin da Shugaba Buhari ya bai wa CBN na takaita yawan kudin da jama’a za su fitar daga asusunsu na banki ba tare da tuntubar Majalisar Tattalin Arziki da kuma ta Zartarwa ba, abu ne da ya saba wa tsarin mulki da saba wa doka a don haka ba shi da iko.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.