• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Maka Buhari A Kotun Koli Kan Batu Canjin Kudi 

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ganduje Ya Amince Da Biyan Miliyan 304 Na Alawus Ga Malaman Jami’ar Gwamnatin Kano

Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano ya maka Shugaba Muhammadu Buhari kara a gaban Kotun Koli kan sauya fasalin da aka yi wa takardun naira.

A watan Oktoban bara ne dai Babban Bankin Najeriya CBN bisa amincewar Shugaba Buhari ya sauya fasalin wasu daga cikin manyan kudin kasar na naira 200 da 500 da 1,000.

  • APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
  • Bayan Shafe Shekaru 32 Yana Limanci A Harami Sheikh Shuraim, Ya Nemi Uzurin Ajiye Limancin

A karar mai lamba SC/CS/200/2023 wadda Babban Lauyan Jihar Kano ya shigar ta hannun Sunusi Musa, Babban Lauya a Najeriya (SAN), Gwamnatin Kano ta ayyana cewa Shugaba Buhari shi kadai ba shi da hurumin umartar CBN dakatar da tsoffin takardun kudin da aka sauyawa fasali.

Aminiya ta ruwaito cewa, karar wadda Gwamnatin Kano ta gabatar a jiya Alhamis, ta kafa hujjar cewa Buhari ba shi da wannan hurumi ba tare da tuntuba da amincewar Majalisar Tattalin Arziki da kuma Majalisar Zartarwa ta kasar ba.

A bisa wannan madogara ce Gwamnatin Kano ta bukaci Kotun Kolin ta soke matakin Babban Bankin na janye takardun kudaden saboda abin ta kira wahalar da al’ummar jihar ke ciki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

A tattaunawarsa da manema labarai, Babban Lauyan da ya shigar da karar Sunusi Musa ya ce a ranar Laraba ne kotun za ta saurari karar.

Kazalika, Gwamnatin Kanon tana son kotun ta bayar da umarnin da zai tilasta wa Gwamnatin Tarayya ta soke shirin nata na sauyin kudi saboda a cewarta ya saba wa Kundin Tsarin Mulkin Kasar na 1999.

An kuma ruwaito cewa Gwamnatin Kanon tana bukatar Kotun Kolin ta zartar cewa umarnin da Shugaba Buhari ya bai wa CBN na takaita yawan kudin da jama’a za su fitar daga asusunsu na banki ba tare da tuntubar Majalisar Tattalin Arziki da kuma ta Zartarwa ba, abu ne da ya saba wa tsarin mulki da saba wa doka a don haka ba shi da iko.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBuhariCanjin KudiCBNGandujeKotun KoliNairaWa'adi
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

Next Post

Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

Related

Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

7 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

20 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

1 day ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

1 day ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

2 days ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

2 days ago
Next Post
Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Tawagar Ba Da Tallafin Jiyya Ta Sin Dake Afrika Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.