ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Sauye-sauyen da ake gani a wani lungu na wani birni ya kan iya nuna ci gaban da daukacin wata kasa ta samu. 

Misali, a yau na raka wani abokina dan Najeriya zuwa ofishin hukumar shige da fice ta birnin Beijing na kasar Sin, domin kula da wasu harkoki, sai na tarar da yadda hukumar ta kaura zuwa wani sabon gini da aka kammala, mai taken “Cibiyar Hidimomin Gwamnati”. A wurin, ana iya kammala ayyukan da suka shafi hidimomi na gwamnati nau’ika sama da 1,900 cikin sauri, ta hanyar nemo tagar da ta dace, da aka kebe wa masu bukatar daidaita mabambantan harkoki. Wato yanzu babu bukatar yin kai-komo tsakanin hukumomi daban-daban, kamar yadda a kan yi a wasu lokuta a baya.

  • Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
  • Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Bari in yi muku karin haske kan taken wannan bayani: “Tsayi” na nufin manyan gine-gine da suke nuna yanayin ci gaba na wani birni, da habakar tattalin arzikinsa. Kana “zafi” a nan ba ya nufin yanayi, maimakon haka yana nufin jin dadi da gamsuwar mutanen da ke zaune a cikin birnin. Kula da wadannan bangarori guda biyu yadda ya kamata, shi ne umarnin da gwamnatin kasar Sin ta gabatar wa jami’ai masu kula da birane 694 na kasar.

ADVERTISEMENT

A yau da ni da abokina mun gama ayyukanmu cikin sauri, mun fito daga Cibiyar Hidimomin Gwamnati, sa’an nan mun waiwayi baya, mun ga cikakken tsarin wannan babban gini mai salon zamani. Abun da muke ji shi ne: Beijing ta samu karin ci gaba. A lokacin, mun shaida “tsayi” na ci gaban birnin Beijing, da kuma “zafi” na birnin a cikin zukatanmu.

Wani taro da ya gudana a baya-bayan nan game da aikin raya birane a kasar Sin, ya ta’allaka ne kan manufar “amfani da tsare-tsaren birane wajen samar da hidimomi ga jama’a”, tare da ba da shawarar raya biranen kasar, don su zama masu sabbin fasahohin da aka kirkira, da ingancin muhallin rayuwa, da kyan gani, da iya tinkarar bala’i, da wayewar kai, gami da basira. Alal hakika, tun tuni an riga an fara aiwatar da wadannan ra’ayoyi a biranen Sin: Tun daga shekarar 2019 har zuwa yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gyaran tsoffin ungwanni kusan 280,000, da kafa na’urorin lif sama da 130,000, da gina karin wuraren ajiye motoci miliyan 3.8, da sabbin filayen motsa jiki da fadinsu ya kai murabba’in mita miliyan 31.

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Har ila yau, Sinawa sun yada irin wannan ra’ayi na raya birane don bautawa jama’a, zuwa nahiyar Afirka . Misali, a Lagos na Najeriya, layin dogo na “Blue Line” da wani kamfanin kasar Sin ya gina ya takaita lokacin zirga-zirgar jama’a da dama, daga minti 90 zuwa minti 20. Kana a birnin Lusaka na kasar Zambia, tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa da wani kamfanin Sin ya gina, ta sa an samu karin hasken fitilu, a shaguna daban daban dake kan titunan birnin a cikin dare.

Ban da haka, a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, aikin kwaskwarima da kamfanonin kasar Sin suka gudanar, sun mayar da wani kango cike da laka zuwa daya daga cikin filayen wasa mafi girma da inganci da ake samu a cikin biranen Afirka.

“Ya kamata a tabbatar da ‘tsayi’, gami da ‘zafi’, yayin da ake raya wani birni.” Bari mu tuna da wannan magana ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, mu kuma shaida yadda sannu a hankali ta zama gaskiya a birane daban daban na kasar Sin da na kasashen Afirka. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su
  • Sulaiman
    An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf
  • Sulaiman
    NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

MASU ALAKA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka
Ra'ayi Riga

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026
Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

September 20, 2026
Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

September 20, 2026
Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

September 20, 2026
Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

September 20, 2026
An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

September 20, 2026
Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

September 20, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

September 20, 2026
Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

September 20, 2026
NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

September 20, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina

September 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.