ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sin

Sauye-sauyen da ake gani a wani lungu na wani birni ya kan iya nuna ci gaban da daukacin wata kasa ta samu. 

Misali, a yau na raka wani abokina dan Najeriya zuwa ofishin hukumar shige da fice ta birnin Beijing na kasar Sin, domin kula da wasu harkoki, sai na tarar da yadda hukumar ta kaura zuwa wani sabon gini da aka kammala, mai taken “Cibiyar Hidimomin Gwamnati”. A wurin, ana iya kammala ayyukan da suka shafi hidimomi na gwamnati nau’ika sama da 1,900 cikin sauri, ta hanyar nemo tagar da ta dace, da aka kebe wa masu bukatar daidaita mabambantan harkoki. Wato yanzu babu bukatar yin kai-komo tsakanin hukumomi daban-daban, kamar yadda a kan yi a wasu lokuta a baya.

  • Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
  • Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Bari in yi muku karin haske kan taken wannan bayani: “Tsayi” na nufin manyan gine-gine da suke nuna yanayin ci gaba na wani birni, da habakar tattalin arzikinsa. Kana “zafi” a nan ba ya nufin yanayi, maimakon haka yana nufin jin dadi da gamsuwar mutanen da ke zaune a cikin birnin. Kula da wadannan bangarori guda biyu yadda ya kamata, shi ne umarnin da gwamnatin kasar Sin ta gabatar wa jami’ai masu kula da birane 694 na kasar.

ADVERTISEMENT

A yau da ni da abokina mun gama ayyukanmu cikin sauri, mun fito daga Cibiyar Hidimomin Gwamnati, sa’an nan mun waiwayi baya, mun ga cikakken tsarin wannan babban gini mai salon zamani. Abun da muke ji shi ne: Beijing ta samu karin ci gaba. A lokacin, mun shaida “tsayi” na ci gaban birnin Beijing, da kuma “zafi” na birnin a cikin zukatanmu.

Wani taro da ya gudana a baya-bayan nan game da aikin raya birane a kasar Sin, ya ta’allaka ne kan manufar “amfani da tsare-tsaren birane wajen samar da hidimomi ga jama’a”, tare da ba da shawarar raya biranen kasar, don su zama masu sabbin fasahohin da aka kirkira, da ingancin muhallin rayuwa, da kyan gani, da iya tinkarar bala’i, da wayewar kai, gami da basira. Alal hakika, tun tuni an riga an fara aiwatar da wadannan ra’ayoyi a biranen Sin: Tun daga shekarar 2019 har zuwa yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gyaran tsoffin ungwanni kusan 280,000, da kafa na’urorin lif sama da 130,000, da gina karin wuraren ajiye motoci miliyan 3.8, da sabbin filayen motsa jiki da fadinsu ya kai murabba’in mita miliyan 31.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Har ila yau, Sinawa sun yada irin wannan ra’ayi na raya birane don bautawa jama’a, zuwa nahiyar Afirka . Misali, a Lagos na Najeriya, layin dogo na “Blue Line” da wani kamfanin kasar Sin ya gina ya takaita lokacin zirga-zirgar jama’a da dama, daga minti 90 zuwa minti 20. Kana a birnin Lusaka na kasar Zambia, tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa da wani kamfanin Sin ya gina, ta sa an samu karin hasken fitilu, a shaguna daban daban dake kan titunan birnin a cikin dare.

Ban da haka, a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, aikin kwaskwarima da kamfanonin kasar Sin suka gudanar, sun mayar da wani kango cike da laka zuwa daya daga cikin filayen wasa mafi girma da inganci da ake samu a cikin biranen Afirka.

“Ya kamata a tabbatar da ‘tsayi’, gami da ‘zafi’, yayin da ake raya wani birni.” Bari mu tuna da wannan magana ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, mu kuma shaida yadda sannu a hankali ta zama gaskiya a birane daban daban na kasar Sin da na kasashen Afirka. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.