Akalla mutum 41 ne suka mutu yayin da wasu 14 suka jikkata sakamakon barkewar wutar gobara a cikin wata Coci da ke birnin Giza a kusa da Cairo, kamar yadda hukumar lafiya ta kasar Egypt ta sanar.
Binciken ‘yansandan kasar ya ce wutar gobarar ta tashi ne sakamakon wutar lantarki.
-  NLC Ta Bukaci Buhari Ya Kara Albashin Ma’aikata Da Kashi 50
- Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
Majiyoyin tsaro biyu sun shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa wutar ta barke ne a daidai lokacin da masu Ibada sama da 5,000 ke gudanar da ibadarsu a cikin majami’ar.
An tura injunan kashe gobara har guda 15 a yayin da kuma wadanda suka jikkata aka kwashe su cikin motar daukar marasa lafiya zuwa asibitocin da ke kusa da wajen.
Shugaban kasar Abdel Fattah el-Sisi ya jajanta wa Kiristocin kasar bisa faruwar wannan lamarin.
Daga baya hukumar kashe gobara ta ce an shawo kan gobarar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp